<?xml version="1.0" encoding="UTF-8"?><rss version="2.0"
	xmlns:content="http://purl.org/rss/1.0/modules/content/"
	xmlns:wfw="http://wellformedweb.org/CommentAPI/"
	xmlns:dc="http://purl.org/dc/elements/1.1/"
	xmlns:atom="http://www.w3.org/2005/Atom"
	xmlns:sy="http://purl.org/rss/1.0/modules/syndication/"
	xmlns:slash="http://purl.org/rss/1.0/modules/slash/"
	>

<channel>
	<title>CEDEAO Archives - Arewa Agenda Hausa</title>
	<atom:link href="https://hausa.arewaagenda.com/tag/cedeao/feed/" rel="self" type="application/rss+xml" />
	<link>https://hausa.arewaagenda.com/tag/cedeao/</link>
	<description>Arewa Labarai Hausa</description>
	<lastBuildDate>Sun, 12 Dec 2021 05:15:29 +0000</lastBuildDate>
	<language>en-US</language>
	<sy:updatePeriod>
	hourly	</sy:updatePeriod>
	<sy:updateFrequency>
	1	</sy:updateFrequency>
	<generator>https://wordpress.org/?v=6.9.4</generator>
	<atom:link rel='hub' href='https://hausa.arewaagenda.com/?pushpress=hub'/>
<site xmlns="com-wordpress:feed-additions:1">229835694</site>	<item>
		<title>Gwamnatin Najeriya na Dab da Kawo Ƙarshen Hare-Haren Ta&#8217;addanci a Arewacin Ƙasar &#8211; Malam Garba Shehu</title>
		<link>https://hausa.arewaagenda.com/kawo-karshen-addanci-arewacin/</link>
					<comments>https://hausa.arewaagenda.com/kawo-karshen-addanci-arewacin/#respond</comments>
		
		<dc:creator><![CDATA[Khadija Garba]]></dc:creator>
		<pubDate>Sun, 12 Dec 2021 05:15:29 +0000</pubDate>
				<category><![CDATA[Taska]]></category>
		<category><![CDATA[abuja]]></category>
		<category><![CDATA[Arewacin]]></category>
		<category><![CDATA[CEDEAO]]></category>
		<category><![CDATA[ECOWAS]]></category>
		<category><![CDATA[Gwamnatin Najeriya]]></category>
		<category><![CDATA[Malam Garba Shehu]]></category>
		<category><![CDATA[Ta'addanci]]></category>
		<guid isPermaLink="false">https://hausa.arewaagenda.com/?p=9657</guid>

					<description><![CDATA[<p>Gwamnatin Najeriya na Dab da Kawo Ƙarshen Hare-Haren Ta&#8217;addanci a Arewacin Ƙasar &#8211; Malam Garba Shehu Gwamnatin Najeriya ta ce tana tana dab da kawo karshen hare-haren ta&#8217;addanci a Arewacin kasar. Mai baiwa Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari shawara kan yada kabarai Malam Garba Shehu ya shaida wa BBC cewa za a hada hannu da masu [&#8230;]</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/kawo-karshen-addanci-arewacin/" data-wpel-link="internal">Gwamnatin Najeriya na Dab da Kawo Ƙarshen Hare-Haren Ta&#8217;addanci a Arewacin Ƙasar &#8211; Malam Garba Shehu</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></description>
										<content:encoded><![CDATA[<p><strong>Gwamnatin Najeriya na Dab da Kawo Ƙarshen Hare-Haren Ta&#8217;addanci a Arewacin Ƙasar &#8211; Malam Garba Shehu</strong></p>
<p>Gwamnatin Najeriya ta ce tana tana dab da kawo karshen hare-haren ta&#8217;addanci a Arewacin kasar.</p>
<p>Mai baiwa Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari shawara kan yada kabarai Malam Garba Shehu ya shaida wa BBC cewa za a hada hannu da masu ruwa da tsaki a ciki da wajen kasar don shawo kan matsalar tsaron.</p>
<p>Dama yau Lahadi ne ake soma taron shugabanin kungiyar ECOWAS ko kuma CEDEAO karo na 60 a Abuja.</p>
<p>Wannan taro zai gudana ne a daidai lokacin da yawancin kasashen na yammacin Afrika ke cikin wani yanayi na tsananin rashin tsaro, lura da yadda kungiyoyin tada kayar baya da sauran &#8216;yan bindiga suka addabe su.</p>
<p>A &#8216;yan kwanakin nan mahara sun kona matafiya sama da 20 a jihar Sokoto da ke arewacin Najeriya, kuma kafin nan wasu maharan sun kona wasu matafiyan da ke hanyarsu ta zuwa cin kasuwa a tsakiyar Mali.</p>
<p>Lamarin ya kara tada hankalin al&#8217;umma tare da haifar da ce-ce-ku-ce, inda ake zargin hukumomin kasashen da nuna gazawa.</p>
<p>A cewar Malam Shehu Garba, mataimaki na musamman ga Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari kan yada labarai, taron ya zo a dai-dai lokacin da ya dace, lura da tarin kalubala da ECOWAS ke fuskanta a kasashe daban-daban.</p>
<p>&#8221; Taro ne a kan gaba. Kowa ya san halin da demokradiyya ta tsinci kanta a kasashen Mali da Guinea. Ga kuma batun rashin tsaro, don ECOWAS ta fahimci cewa &#8216;yan tada kayar baya ketarawa suke yi iyakokin makwabtan kasashe, saboda haka babu wata kasa da za ta ware kanta ta yi wannan yaki. Dole ne a hadu a yi yaki tare,&#8221; in ji Garba Shehu.</p>
<p>Kan karuwar hare-hare da satar jama&#8217;a a Arewacin Najeriya, Malam Garba Shehu ya ce, &#8221; Shugaban kasa ya tura wakilci na musamman na masu ruwa da tsaki a sha&#8217;anin tsaron kasa musamman samar da bayanan sirri, kuma sun je sun tattauna da wakilai a matakin kananan hukumomi da jihohi sun dawo masa da rahoto, kuma za a ga abin da zai biyo baya.&#8221;</p>
<p>Kazalika ya ce a matakin kasa da kasa, taron na ECOWAS ko kuma CEDEAO zai ba da tasa gudummuwa wurin kawo karshen hare-hare a Arewacin Najeriyar.</p>
<p>&#8221; Wannan batu yana daya daga cikin ajanda da Shugabanni za su tattauna. Abu ne da ya damu kowa, ba a jin dadi, kuma babu wani Shugaban kasa da za a ce hankalinsa ya kwanta da wannan fitina da ake fama da ita. Saboda haka za a dauki mataki nan ba da jimawa ba za a kawo karshen hare-hare a arewacin Najeriya din-din-din.&#8221; In ji Garba Shehu.</p>
<p>A farkon mako kungiyar bincike kan sha&#8217;anin tsaro a Najeriya ta Beacon Consultants ta fitar da rahoton da ke cewa mahara sun kashe mutum sama da 400 a watan Nuwamba da ya gabata a arewacin Najeriyar.</p>
<p>Baya ga wannan rahoton ya ce sace-sacen jama&#8217;a ya karu a yankin da kusan kashi 40 cikin 100, duk da ya ce matakan dakile hare-haren na aiki a wasu yankunan kasar.</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/kawo-karshen-addanci-arewacin/" data-wpel-link="internal">Gwamnatin Najeriya na Dab da Kawo Ƙarshen Hare-Haren Ta&#8217;addanci a Arewacin Ƙasar &#8211; Malam Garba Shehu</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></content:encoded>
					
					<wfw:commentRss>https://hausa.arewaagenda.com/kawo-karshen-addanci-arewacin/feed/</wfw:commentRss>
			<slash:comments>0</slash:comments>
		
		
		<post-id xmlns="com-wordpress:feed-additions:1">9657</post-id>	</item>
	</channel>
</rss>

<!--
Performance optimized by W3 Total Cache. Learn more: https://www.boldgrid.com/w3-total-cache/?utm_source=w3tc&utm_medium=footer_comment&utm_campaign=free_plugin

Page Caching using Disk: Enhanced 

Served from: hausa.arewaagenda.com @ 2026-05-04 20:15:39 by W3 Total Cache
-->