<?xml version="1.0" encoding="UTF-8"?><rss version="2.0"
	xmlns:content="http://purl.org/rss/1.0/modules/content/"
	xmlns:wfw="http://wellformedweb.org/CommentAPI/"
	xmlns:dc="http://purl.org/dc/elements/1.1/"
	xmlns:atom="http://www.w3.org/2005/Atom"
	xmlns:sy="http://purl.org/rss/1.0/modules/syndication/"
	xmlns:slash="http://purl.org/rss/1.0/modules/slash/"
	>

<channel>
	<title>Godwin Obaseki Archives - Arewa Agenda Hausa</title>
	<atom:link href="https://hausa.arewaagenda.com/tag/godwin-obaseki/feed/" rel="self" type="application/rss+xml" />
	<link>https://hausa.arewaagenda.com/tag/godwin-obaseki/</link>
	<description>Arewa Labarai Hausa</description>
	<lastBuildDate>Thu, 16 Jun 2022 14:17:33 +0000</lastBuildDate>
	<language>en-US</language>
	<sy:updatePeriod>
	hourly	</sy:updatePeriod>
	<sy:updateFrequency>
	1	</sy:updateFrequency>
	<generator>https://wordpress.org/?v=7.0.1</generator>
	<atom:link rel='hub' href='https://hausa.arewaagenda.com/?pushpress=hub'/>
<site xmlns="com-wordpress:feed-additions:1">229835694</site>	<item>
		<title>Jawabin Atiku Abubakar a Wurin Taron Gabatar da Okowa</title>
		<link>https://hausa.arewaagenda.com/jawabin-atiki-gabatar-okowa/</link>
					<comments>https://hausa.arewaagenda.com/jawabin-atiki-gabatar-okowa/#respond</comments>
		
		<dc:creator><![CDATA[Khadija Garba]]></dc:creator>
		<pubDate>Thu, 16 Jun 2022 14:17:33 +0000</pubDate>
				<category><![CDATA[SIYASA]]></category>
		<category><![CDATA[Atiku Abubakar]]></category>
		<category><![CDATA[Bala Muhammad]]></category>
		<category><![CDATA[Emmanuel Udom]]></category>
		<category><![CDATA[Godwin Obaseki]]></category>
		<category><![CDATA[Ifeanyi Okowa]]></category>
		<category><![CDATA[Nyesom Wike]]></category>
		<category><![CDATA[PDP]]></category>
		<category><![CDATA[samuel ortom]]></category>
		<guid isPermaLink="false">https://hausa.arewaagenda.com/?p=10626</guid>

					<description><![CDATA[<p>Jawabin Atiku Abubakar a Wurin Taron Gabatar da Okowa Ba a ga jigon jam&#8217;iyyar PDP kuma gwamnan Jihar Rivers, Nyesom Wike, a bikin gabatar da takwararsa na Jihar Delta, Ifeanyi Okowa, a matsayin dan takarar mataimakin shugaban kasa na PDP a zaben 2023, rahoton Leadership. Idan za a iya tunawa Wike na ya zo na [&#8230;]</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/jawabin-atiki-gabatar-okowa/" data-wpel-link="internal">Jawabin Atiku Abubakar a Wurin Taron Gabatar da Okowa</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></description>
										<content:encoded><![CDATA[<p><strong>Jawabin Atiku Abubakar a Wurin Taron Gabatar da Okowa</strong></p>
<p>Ba a ga jigon jam&#8217;iyyar PDP kuma gwamnan Jihar Rivers, Nyesom Wike, a bikin gabatar da takwararsa na Jihar Delta, Ifeanyi Okowa, a matsayin dan takarar mataimakin shugaban kasa na PDP a zaben 2023, rahoton Leadership.</p>
<p>Idan za a iya tunawa Wike na ya zo na biyu a zaben fidda gwani na shugaban kasa na PDP da aka yi a ranar 28 na watan Mayu inda ya samu kuri&#8217;u 237 yayin da Atiku ya samu kuri&#8217;u 371.</p>
<p>Tun bayan zaben fidda gwanin, ana ta hasashen cewa Wike ne zai zama dan takarar mataimakin shugaban kasa ga Atiku saboda karfin kafa aji da ya ke da shi a jam&#8217;iyyar.</p>
<p>Amma, Okowo ne aka gabatar a matsayin dan takarar mataimakin shugaban kasa na jam&#8217;iyyar ta PDP inda jiga-jigan jam&#8217;iyyar suka hallara a hedkwatarta a Abuja.</p>
<p>Ya ce wani abu da aka duba wurin zaben Okowa shine dacewarsa ya zama magajinsa idan an zabe shi shugaban kasa a 2023</p>
<p>Jawabin Atiku Abubakar wurin taron gabatar da Okowa</p>
<p>&#8220;Na yi murnar sanar da Gwamna Ifeanyi A. Okowa a matsayin mataimaki na. Ina fatan jagorancin kasar mu tare, tare da yan Najeriya don gina gaba mai kyau gare mu baki daya,&#8221; in ji Atiku.</p>
<p>Baya ga shugaban jam&#8217;iyyar na kasa Dr Iyorchia Ayu, mambobin kwamitin ayyuka, NWC, mambobin kwamtin amintattu, BOT, jiga-jigan jam&#8217;iyyar da takwarorin Okowa sun hallarci taron.</p>
<p>Sun hada da gwamnonin jihohin Enugu, Ifeanyi Uguanyi, Bauchi, Bala Mohamemd; Akwa Ibom, Udom Emmanuel; Edo, Godwin Obaseki, da Benue; Samuel Ortom.</p>
<p>Saurari karin bayani &#8230;</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/jawabin-atiki-gabatar-okowa/" data-wpel-link="internal">Jawabin Atiku Abubakar a Wurin Taron Gabatar da Okowa</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></content:encoded>
					
					<wfw:commentRss>https://hausa.arewaagenda.com/jawabin-atiki-gabatar-okowa/feed/</wfw:commentRss>
			<slash:comments>0</slash:comments>
		
		
		<post-id xmlns="com-wordpress:feed-additions:1">10626</post-id>	</item>
		<item>
		<title>Gwamna Obaseki ya Kori Ma&#8217;aikata 513 Daga Bakin Aiki</title>
		<link>https://hausa.arewaagenda.com/obaseki-kori-maaikata-513/</link>
					<comments>https://hausa.arewaagenda.com/obaseki-kori-maaikata-513/#respond</comments>
		
		<dc:creator><![CDATA[Khadija Garba]]></dc:creator>
		<pubDate>Thu, 24 Mar 2022 15:35:54 +0000</pubDate>
				<category><![CDATA[SIYASA]]></category>
		<category><![CDATA[Edo]]></category>
		<category><![CDATA[Godwin Obaseki]]></category>
		<category><![CDATA[Ma'aikata]]></category>
		<guid isPermaLink="false">https://hausa.arewaagenda.com/?p=9983</guid>

					<description><![CDATA[<p>Gwamna Obaseki ya Kori Ma&#8217;aikata 513 Daga Bakin Aiki &#160; Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki, ya amince da korar ma&#8217;aikata 513 daga bakin aiki waɗan da ke sashin harkokin wasanni. A wani kundi mai ɗauke da sanarwan korar ma&#8217;aikatan, gwamnan ya ce ya ɗauki wannan matakin domin garambawul ga sashin. Ma&#8217;aikatan da korar ta shafa [&#8230;]</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/obaseki-kori-maaikata-513/" data-wpel-link="internal">Gwamna Obaseki ya Kori Ma&#8217;aikata 513 Daga Bakin Aiki</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></description>
										<content:encoded><![CDATA[<p><strong>Gwamna Obaseki ya Kori Ma&#8217;aikata 513 Daga Bakin Aiki</strong></p>
<p>&nbsp;</p>
<p>Gwamnan jihar Edo, Godwin Obaseki, ya amince da korar ma&#8217;aikata 513 daga bakin aiki waɗan da ke sashin harkokin wasanni.</p>
<p>A wani kundi mai ɗauke da sanarwan korar ma&#8217;aikatan, gwamnan ya ce ya ɗauki wannan matakin domin garambawul ga sashin.</p>
<p>Ma&#8217;aikatan da korar ta shafa da suka haɗa da yan wasa da masu horarwa da shugabanni, sun fantsama tituna suna zanga-zanga ranar Laraba.</p>
<p>Edo- Gwamna Godwin Obaseki na jihar Edo, ya sallami ma&#8217;aikata 513 na sashin wasanni na jihar kuma matakin ya fara aiki tun daga Litinin 21 ga watan Maris, 2022.</p>
<p>Sallamar aikin a cewar rahoton Vanguard, na cikin wata sanarwa da gwamnatin ta fitar ranar 4 ga watan Maris, 2022, kuma waɗan da lamarin ya shafa ya kunshi manya da ƙananan ma&#8217;aikata.</p>
<p>Legit.ng Hausa ta gano gwamnatin na cewa matakin wani bangare ne na kokarin da take na canza salon sashin wasanni zuwa hukumar wasanni ta jihar Edo.</p>
<p>Zamu biya ma&#8217;aikatan da aka kora haƙƙinsu &#8211; Gwmanati</p>
<p>Sanarwan ta ƙara da cewa gwamnati zata biya ma&#8217;ikatan da korar ta shafa hakkokinsu na albashin wata ɗaya.</p>
<p>Hakanan ta ce za&#8217;a fara biyan ma&#8217;aikatan kuɗin Fanshon su a watan Afrilu, 2020, a rahoton Leadership ma&#8217;ikatan da aka sallama sun kai 514.</p>
<p>Ma&#8217;aikatan da matakin sallamar ya shafa sun haɗa da, yan wasan guje-guje da tsalle-tsalle, masu horarwa da kuma na ɓangaren shugabanci.</p>
<p>Wane mataki ma&#8217;aikatan suka ɗauka?</p>
<p>A ranar 24 ga watan Maris, 2022, ma&#8217;aikatan da gwamnan ya kora suka fito gagarumar zanga-zanga a kewayen filin Samuel Ogbemudia da wasu tituna dake kusa.</p>
<p>Wasu daga cikin mutanen sun ce sun yi mamakin ganin sanarwan cewa an sallame su daga aiki, kuma aka ba su shawaran su sake neman aiki na wucin gadi.</p>
<p>Ɗaya daga cikin yan zanga-zangan, Patience Igbiti, ta ce:</p>
<p>&#8220;Sama da shekara 20 ina aiki a matsayin cikakkiyar ma&#8217;aikaciya kuma lokaci guda suka kore ni. Na ƙi karban ayyuka da dama a ƙasar waje domin na yi wa jihata aiki. Daga ina ake son na fara yanzu?&#8221;</p>
<p>Haka nan kuma wani ma&#8217;aikacin da lamarin ya shafa, Friday Aibangbe, ya ce:</p>
<p>&#8220;Ina da kwarin guiwar cewa gwamna bai damu da mu ba kwata-kwata. Mun masa aiki muka zaɓe shi kuma muka sadaukar domin shi, amma abin da ya saka mana da shi kenan yanzu.&#8221;</p>
<p>Da yake jawabi ga masu zanga-zanga, shugaban hukumar wasanni, Yusuf Ali, ya ɗau alƙawarin kai korafinsu ga gwamnatin jiha.</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/obaseki-kori-maaikata-513/" data-wpel-link="internal">Gwamna Obaseki ya Kori Ma&#8217;aikata 513 Daga Bakin Aiki</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></content:encoded>
					
					<wfw:commentRss>https://hausa.arewaagenda.com/obaseki-kori-maaikata-513/feed/</wfw:commentRss>
			<slash:comments>0</slash:comments>
		
		
		<post-id xmlns="com-wordpress:feed-additions:1">9983</post-id>	</item>
		<item>
		<title>Gwamnonin Yankin Kudu Maso Kudu Sun Shiga Taro a Gidan Gwamnatin Jahar Ribas</title>
		<link>https://hausa.arewaagenda.com/gwamnonin-kudu-shiga-taro/</link>
					<comments>https://hausa.arewaagenda.com/gwamnonin-kudu-shiga-taro/#respond</comments>
		
		<dc:creator><![CDATA[Khadija Garba]]></dc:creator>
		<pubDate>Mon, 04 Oct 2021 12:31:01 +0000</pubDate>
				<category><![CDATA[SIYASA]]></category>
		<category><![CDATA[Edo]]></category>
		<category><![CDATA[Godwin Obaseki]]></category>
		<category><![CDATA[gwamnoni]]></category>
		<category><![CDATA[Kudu Maso Kudu]]></category>
		<category><![CDATA[Nyesom Wike]]></category>
		<category><![CDATA[Ribas]]></category>
		<category><![CDATA[VAT]]></category>
		<guid isPermaLink="false">https://hausa.arewaagenda.com/?p=8778</guid>

					<description><![CDATA[<p>Gwamnonin Yankin Kudu Maso Kudu Sun Shiga Taro a Gidan Gwamnatin Jahar Ribas &#160; A halin yanzu gwamnonin jahohi shida na shiyyar siyasar yankin Kudu-maso-Kudu suna taro a gidan gwamnatin jahar Ribas da ke Fatakwal. Ko da yake ba a san dalilin taron ba tukuna, wakilin Punch ya ba da rahoton cewa lamuran harajin VAT [&#8230;]</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/gwamnonin-kudu-shiga-taro/" data-wpel-link="internal">Gwamnonin Yankin Kudu Maso Kudu Sun Shiga Taro a Gidan Gwamnatin Jahar Ribas</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></description>
										<content:encoded><![CDATA[<p><strong>Gwamnonin Yankin Kudu Maso Kudu Sun Shiga Taro a Gidan Gwamnatin Jahar Ribas</strong></p>
<p>&nbsp;</p>
<p>A halin yanzu gwamnonin jahohi shida na shiyyar siyasar yankin Kudu-maso-Kudu suna taro a gidan gwamnatin jahar Ribas da ke Fatakwal.</p>
<p>Ko da yake ba a san dalilin taron ba tukuna, wakilin Punch ya ba da rahoton cewa lamuran harajin VAT da Shugabancin Kudanci a 2023 na daga cikin abubuwan da za su caccaka tsinke a tattaunawar.</p>
<p>An ga gwamna mai masaukin baki, Nyesom Wike, da Gwamna Godwin Obaseki na Edo, suna ta hira a wurin taron.</p>
<p>Karin bayani nan tafe..</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/gwamnonin-kudu-shiga-taro/" data-wpel-link="internal">Gwamnonin Yankin Kudu Maso Kudu Sun Shiga Taro a Gidan Gwamnatin Jahar Ribas</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></content:encoded>
					
					<wfw:commentRss>https://hausa.arewaagenda.com/gwamnonin-kudu-shiga-taro/feed/</wfw:commentRss>
			<slash:comments>0</slash:comments>
		
		
		<post-id xmlns="com-wordpress:feed-additions:1">8778</post-id>	</item>
		<item>
		<title>Rigakafin Corona: Dokar Dakatar da Ma&#8217;aikatan da Basu da Katin Shaida ta Fara Aiki a Jahar Edo</title>
		<link>https://hausa.arewaagenda.com/katin-shaida-ragakfin-corona/</link>
					<comments>https://hausa.arewaagenda.com/katin-shaida-ragakfin-corona/#respond</comments>
		
		<dc:creator><![CDATA[Khadija Garba]]></dc:creator>
		<pubDate>Wed, 15 Sep 2021 13:01:27 +0000</pubDate>
				<category><![CDATA[Taska]]></category>
		<category><![CDATA[Edo]]></category>
		<category><![CDATA[Godwin Obaseki]]></category>
		<category><![CDATA[Rigakafin Corona]]></category>
		<guid isPermaLink="false">https://arewaagenda.com/hausa/?p=7964</guid>

					<description><![CDATA[<p>Rigakafin Corona: Dokar Dakatar da Ma&#8217;aikatan da Basu da Katin Shaida ta Fara Aiki a Jahar Edo &#160; Jami&#8217;an lafiya tare da haɗin kan jami&#8217;an tsaro sun fara aiwatar da umarnin gwamnan jahar Edo, Godwin Obaseki kan rigakafin corona. Gwamnan ya sanar da shirin gwamnatinsa na dakatar da duk wani ma&#8217;aikaci da bai yi allurar [&#8230;]</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/katin-shaida-ragakfin-corona/" data-wpel-link="internal">Rigakafin Corona: Dokar Dakatar da Ma&#8217;aikatan da Basu da Katin Shaida ta Fara Aiki a Jahar Edo</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></description>
										<content:encoded><![CDATA[<p><strong>Rigakafin Corona: Dokar Dakatar da Ma&#8217;aikatan da Basu da Katin Shaida ta Fara Aiki a Jahar Edo</strong></p>
<p>&nbsp;</p>
<p>Jami&#8217;an lafiya tare da haɗin kan jami&#8217;an tsaro sun fara aiwatar da umarnin gwamnan jahar Edo, Godwin Obaseki kan rigakafin corona.</p>
<p>Gwamnan ya sanar da shirin gwamnatinsa na dakatar da duk wani ma&#8217;aikaci da bai yi allurar rigakafin COVID19 ba daga zuwa aiki.</p>
<p>Wasu hotuna da suka fito daga jahar sun bayyana yadda ma&#8217;aikata ke nuna katin shaida kafin shiga kowace ma&#8217;aikata a Benin.</p>
<p>Edo &#8211; Gwamnatin jahar Edo, karkashin jagorancin gwamna Obaseki ta fara aiwatar da dokar &#8220;Ba rigafin korona, babu aiki&#8221; a ma&#8217;aikatun jahar, kamar yadda dailytrust ta rawaito.</p>
<p>Gwamna Obaseki na jahar Edo, shine gwamna na farko a Najeriya da ya hana mutanen da ba&#8217;a musu rigakafin cutar COVID19 ba shiga wuraren gwamnati.</p>
<p>Duk da cewa da farko an yi watsi da kudirin gwamnan, amma Obaseki bai yi kasa a guiwa ba wajen aiwatar da kudirinsa.</p>
<p>Su wa ke hana mutane shiga ma&#8217;aikatu?</p>
<p>A ranar Laraba da safe, jami&#8217;an lafiya da kuma jami&#8217;an tsaro sun kafa madakata a kofar shiga ma&#8217;aikatun Benin, Babban birnin jahar, inda suke tabbatar da an bi umarnin gwamna.</p>
<p>Ba damar shiga sakateriyar gwamnati a Edo sai da kati</p>
<p>Punch ta rawaito cewa an hana duk wani ma&#8217;aikaci da ya gaza gabatar da katin shaidar allurar rigakafin COVID19 shiga sakateriyar gwamnatin Edo.</p>
<p>Gwamnatin ta fara aiwatar da shirinta na hana taruwar mutane da yawa ba tare da shaidar karɓar rigakafi ba.</p>
<p>Lamarin wanda ya fara da karfe 7:00 na safiyar Laraba, yasa an hang shugaban kwamitin yaƙi da COVID19 na jahar, Yusuf Haruna, ya tare babbar kofar shiga sakateriyar wacce ta yi hannun riga da ofishin EFCC.</p>
<p>&nbsp;</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/katin-shaida-ragakfin-corona/" data-wpel-link="internal">Rigakafin Corona: Dokar Dakatar da Ma&#8217;aikatan da Basu da Katin Shaida ta Fara Aiki a Jahar Edo</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></content:encoded>
					
					<wfw:commentRss>https://hausa.arewaagenda.com/katin-shaida-ragakfin-corona/feed/</wfw:commentRss>
			<slash:comments>0</slash:comments>
		
		
		<post-id xmlns="com-wordpress:feed-additions:1">7964</post-id>	</item>
		<item>
		<title>Gwamnatin Edo za ta Haramtawa Wadanda ba a yi wa Rigakafin Corona ba Shiga Bankuna, Ofisoshin Gwamnati da Wuraren Ibada</title>
		<link>https://hausa.arewaagenda.com/rigakafin-corona-shiga-wurare/</link>
					<comments>https://hausa.arewaagenda.com/rigakafin-corona-shiga-wurare/#respond</comments>
		
		<dc:creator><![CDATA[Khadija Garba]]></dc:creator>
		<pubDate>Tue, 14 Sep 2021 19:22:34 +0000</pubDate>
				<category><![CDATA[Taska]]></category>
		<category><![CDATA[Corona]]></category>
		<category><![CDATA[Edo]]></category>
		<category><![CDATA[Godwin Obaseki]]></category>
		<guid isPermaLink="false">https://arewaagenda.com/hausa/?p=7888</guid>

					<description><![CDATA[<p>Gwamnatin Edo za ta Haramtawa Wadanda ba a yi wa Rigakafin Corona ba Shiga Bankuna, Ofisoshin Gwamnati da Wuraren Ibada &#160; Jahar Edo &#8211; Gwamnatin Jahar Edo ta haramtawa ma&#8217;aikatan da ba su yi allurar riga-kafin corona ba shiga ofishosinsu kamar yadda Daily Trust ta rawaito. Gwamnatin ta hana dukkan wadanda ba su riga sun [&#8230;]</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/rigakafin-corona-shiga-wurare/" data-wpel-link="internal">Gwamnatin Edo za ta Haramtawa Wadanda ba a yi wa Rigakafin Corona ba Shiga Bankuna, Ofisoshin Gwamnati da Wuraren Ibada</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></description>
										<content:encoded><![CDATA[<p><strong>Gwamnatin Edo za ta Haramtawa Wadanda ba a yi wa Rigakafin Corona ba Shiga Bankuna, Ofisoshin Gwamnati da Wuraren Ibada</strong></p>
<p>&nbsp;</p>
<p>Jahar Edo &#8211; Gwamnatin Jahar Edo ta haramtawa ma&#8217;aikatan da ba su yi allurar riga-kafin corona ba shiga ofishosinsu kamar yadda Daily Trust ta rawaito.</p>
<p>Gwamnatin ta hana dukkan wadanda ba su riga sun yi riga-kafin ba shiga wuraren taruwan mutane.</p>
<p>Tunda farko, Gwamna Godwin Obaseki, a cikin watan Satumba, ya hana wadanda ba a yi wa rigakafi shiga bankuna, ofisoshin gwamnati da wuraren ibada.</p>
<p>Hakan ya janyo cece-kuce inda wata kungiya ta tafi domin hana aiwatar da dokar amma gwamnan bai sauya ra&#8217;ayinsa ba.</p>
<p>A ranar Talata, sakataren dindindin na ma&#8217;aikatar lafiya na jahar Edo, Osamwonyi Irowa, ya ce daga ranar 15 watan Satumban 2021 ya ce gwamnatin za ta aiwatar da dokar &#8216;babu katin riga-kafi, ba shiga wuraren taruwan jama&#8217;a&#8217;.</p>
<p>Ku saurari karin bayani &#8230;</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/rigakafin-corona-shiga-wurare/" data-wpel-link="internal">Gwamnatin Edo za ta Haramtawa Wadanda ba a yi wa Rigakafin Corona ba Shiga Bankuna, Ofisoshin Gwamnati da Wuraren Ibada</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></content:encoded>
					
					<wfw:commentRss>https://hausa.arewaagenda.com/rigakafin-corona-shiga-wurare/feed/</wfw:commentRss>
			<slash:comments>0</slash:comments>
		
		
		<post-id xmlns="com-wordpress:feed-additions:1">7888</post-id>	</item>
		<item>
		<title>&#8216;Yan Bindiga Sun yi Garkuwa da Jigon PDP na Jahar Edo, Owere Dickson</title>
		<link>https://hausa.arewaagenda.com/yanbindiga-garkuwa-jigon-pdp/</link>
					<comments>https://hausa.arewaagenda.com/yanbindiga-garkuwa-jigon-pdp/#respond</comments>
		
		<dc:creator><![CDATA[Khadija Garba]]></dc:creator>
		<pubDate>Mon, 13 Sep 2021 13:27:50 +0000</pubDate>
				<category><![CDATA[SIYASA]]></category>
		<category><![CDATA[Edo]]></category>
		<category><![CDATA[Godwin Obaseki]]></category>
		<category><![CDATA[Owere Dickson]]></category>
		<category><![CDATA[PDP]]></category>
		<guid isPermaLink="false">https://arewaagenda.com/hausa/?p=7805</guid>

					<description><![CDATA[<p>&#8216;Yan Bindiga Sun yi Garkuwa da Jigon PDP na Jahar Edo, Owere Dickson &#160; Rahotanni sun bayyana cewa an sace wani jigon jam’iyyar PDP kuma jagoran jam’iyyar a gundumar Sanatan Edo ta Kudu, Owere Dickson Imasogie tare da direban sa a safiyar yau. An yi garkuwa da jigon ne a kan hanyarsa ta zuwa gonarsa [&#8230;]</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/yanbindiga-garkuwa-jigon-pdp/" data-wpel-link="internal">&#8216;Yan Bindiga Sun yi Garkuwa da Jigon PDP na Jahar Edo, Owere Dickson</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></description>
										<content:encoded><![CDATA[<p><strong>&#8216;Yan Bindiga Sun yi Garkuwa da Jigon PDP na Jahar Edo, Owere Dickson</strong></p>
<p>&nbsp;</p>
<p>Rahotanni sun bayyana cewa an sace wani jigon jam’iyyar PDP kuma jagoran jam’iyyar a gundumar Sanatan Edo ta Kudu, Owere Dickson Imasogie tare da direban sa a safiyar yau.</p>
<p>An yi garkuwa da jigon ne a kan hanyarsa ta zuwa gonarsa lokacin da wasu da ake zargin masu garkuwa da mutane suka kama shi da misalin karfe 7 na safe, The Sun ta rawaito.</p>
<p>Wata majiya kusa da danginsa ta ce:</p>
<p>“An yi garkuwa da shi a gonarsa da ke kewayen yankin Obada a karamar hukumar Uhunmwonde. Yana tare da direbansa lokacin da lamarin ya faru.&#8221;</p>
<p>A lokacin shigar da wannan rahoto, rundunar ‘yan sanda ba ta tabbatar ko ta yi wani bayani kan lamarin ba amma wata kungiya, Edo State Decide Movement, a cikin wata sanarwa, ta yi kira ga gwamnan jahar, Godwin Obaseki da ya ceto Owere Dickson.</p>
<p>A wani bangare na sanarwar, kungiyar ta ce:</p>
<p>“Cikin gaggawa, muna kira ga gwamnatin jahar ta Godwin Obaseki da ta dauki kwakkwaran mataki na ceto uban ga kowa da kowa daga hannun &#8216;yan bindiga ko masu garkuwa da mutane wadanda makiyan ci gaba ne a jahar mu mai kaunar ci gaba.&#8221;</p>
<p>Karin bayani na nan tafe..</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/yanbindiga-garkuwa-jigon-pdp/" data-wpel-link="internal">&#8216;Yan Bindiga Sun yi Garkuwa da Jigon PDP na Jahar Edo, Owere Dickson</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></content:encoded>
					
					<wfw:commentRss>https://hausa.arewaagenda.com/yanbindiga-garkuwa-jigon-pdp/feed/</wfw:commentRss>
			<slash:comments>0</slash:comments>
		
		
		<post-id xmlns="com-wordpress:feed-additions:1">7805</post-id>	</item>
		<item>
		<title>Atiku Abubakar da Gwamna Obaseki Sun Hada Gwiwa Don Kayar da Jam&#8217;iyyar APC a 2023</title>
		<link>https://hausa.arewaagenda.com/atiku-obaseki-kayar-apc/</link>
					<comments>https://hausa.arewaagenda.com/atiku-obaseki-kayar-apc/#respond</comments>
		
		<dc:creator><![CDATA[Khadija Garba]]></dc:creator>
		<pubDate>Tue, 24 Aug 2021 12:18:32 +0000</pubDate>
				<category><![CDATA[SIYASA]]></category>
		<category><![CDATA[2023]]></category>
		<category><![CDATA[APC]]></category>
		<category><![CDATA[Atiku Abubakar]]></category>
		<category><![CDATA[benue]]></category>
		<category><![CDATA[Godwin Obaseki]]></category>
		<category><![CDATA[PDP]]></category>
		<guid isPermaLink="false">https://arewaagenda.com/hausa/?p=6845</guid>

					<description><![CDATA[<p>Atiku Abubakar da Gwamna Obaseki Sun Hada Gwiwa Don Kayar da Jam&#8217;iyyar APC a 2023 &#160; Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar, ya ce tarurrukan sulhu da ke gudana tsakanin shugabannin PDP na samun sakamako mai kyau. Abubakar ya bayyana haka a Benin, babban birnin jahar Edo, a ranar Litinin, 23 ga watan Agusta, bayan [&#8230;]</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/atiku-obaseki-kayar-apc/" data-wpel-link="internal">Atiku Abubakar da Gwamna Obaseki Sun Hada Gwiwa Don Kayar da Jam&#8217;iyyar APC a 2023</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></description>
										<content:encoded><![CDATA[<p><strong>Atiku Abubakar da Gwamna Obaseki Sun Hada Gwiwa Don Kayar da Jam&#8217;iyyar APC a 2023</strong></p>
<p>&nbsp;</p>
<p>Tsohon mataimakin shugaban Najeriya, Atiku Abubakar, ya ce tarurrukan sulhu da ke gudana tsakanin shugabannin PDP na samun sakamako mai kyau.</p>
<p>Abubakar ya bayyana haka a Benin, babban birnin jahar Edo, a ranar Litinin, 23 ga watan Agusta, bayan ganawa da gwamna Obaseki.</p>
<p>A cewarsa, za a karfafa babbar jam&#8217;iyyar adawa a kasar don karbe mulki a 2023 daga APC.</p>
<p>Benin, Edo &#8211; Tsohon mataimakin shugaban kasa Atiku Abubakar a ranar Litinin, 23 ga watan Agusta ya ayyana cewa jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) tana da kyakkyawan matsayi yanzu don kawar da jam’iyyar All Progressives Congress (APC) mai mulki daga mulki a 2023.</p>
<p>The News ta ruwaito cewa Atiku ya bayyana hakan a Benin, babban birnin jahar Edo, inda ya kara da cewa ziyarar wani bangare ne na shawarwari kan yadda za a karfafa PDP don karbe mulki daga hannun APC gabanin zaben shugaban kasa na 2023.</p>
<p>Legit.ng ta tattaro cewa Atiku ya shaidawa manema labarai bayan ganawar cewa tattaunawarsa da gwamna Obaseki ya ta&#8217;allaka ne kan mulki, yanayin da kasar ke ciki da kuma yadda za a karfafa jam&#8217;iyyar PDP don karbe madafun iko a shekarar 2023.</p>
<p>Ya ce:</p>
<p>&#8220;Musamman, mun tattauna game da shugabanci, halin da ake ciki a ƙasar, mun tattauna game da jam&#8217;iyyarmu, yadda yakamata a ƙarfafa jam&#8217;iyyarmu da kuma karɓar jagoranci a jahohi da dama da kuma gwamnatin tarayya.&#8221;</p>
<p>Obaseki yayi kira da a sake gina PDP kafin zaben shugaban kasa na 2023</p>
<p>Gwamna Obaseki ya kuma ce akwai bukatar sake gina babbar jam’iyyar PDP gabanin zaben shugaban kasa na 2023 domin ceto Najeriya daga matsalolin da take fuskanta.</p>
<p>Obaseki ya ce:</p>
<p>&#8220;Dole ne mu baiwa &#8216;yan Najeriya kwarin gwiwa, halin da muke gani a kasashe da dama masu rauni, bayan barkewar cutar ba ta da kyau ko kadan.</p>
<p>&#8220;Da farko, muna buƙatar gina wata jam’iyya mai ƙarfi don ceto Najeriya, na kasance a gefe guda, a bayyane yake cewa akwai jam&#8217;iyya ɗaya a Najeriya, wanda ita ce PDP.&#8221;</p>
<p>Obaseki ya bayyana abin da ya kira karancin abinci mai zuwa da tsadar kayan abinci a matsayin abin tsoro mafi girma a kasar.</p>
<p>Ya kara da cewa a halin yanzu kasar na cikin mawuyacin hali na tattalin arziki a tarihin kasancewarta kasa.</p>
<p>Jaridar The Nation ta kuma rawaito cewa Obaseki ya jinjinawa Atiku saboda gudunmawar da ya bayar wajen cigaban dimokradiyya.</p>
<p>Ya gode wa Atiku kan kyakkyawan jagoranci, shawarwarin da ya ba shi a lokacin zabensa, ya kara da cewa tsohon mataimakin shugaban kasar ya tattauna ta sirri, kuma ya taimaka masa lokacin da shi da magoya bayansa suka bar APC zuwa PDP.</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/atiku-obaseki-kayar-apc/" data-wpel-link="internal">Atiku Abubakar da Gwamna Obaseki Sun Hada Gwiwa Don Kayar da Jam&#8217;iyyar APC a 2023</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></content:encoded>
					
					<wfw:commentRss>https://hausa.arewaagenda.com/atiku-obaseki-kayar-apc/feed/</wfw:commentRss>
			<slash:comments>0</slash:comments>
		
		
		<post-id xmlns="com-wordpress:feed-additions:1">6845</post-id>	</item>
		<item>
		<title>Zamu Saka Tsauraran Matakai Kan Wanda Basu yi Rigakafin Corona ba &#8211; Gwamatin Jahar Edo</title>
		<link>https://hausa.arewaagenda.com/tsauraran-matakai-rigakafin-corona/</link>
					<comments>https://hausa.arewaagenda.com/tsauraran-matakai-rigakafin-corona/#respond</comments>
		
		<dc:creator><![CDATA[Khadija Garba]]></dc:creator>
		<pubDate>Mon, 23 Aug 2021 19:34:49 +0000</pubDate>
				<category><![CDATA[SIYASA]]></category>
		<category><![CDATA[Astrazeneca]]></category>
		<category><![CDATA[Corona]]></category>
		<category><![CDATA[Edo]]></category>
		<category><![CDATA[Godwin Obaseki]]></category>
		<guid isPermaLink="false">https://arewaagenda.com/hausa/?p=6817</guid>

					<description><![CDATA[<p>Zamu Saka Tsauraran Matakai Kan Wanda Basu yi Rigakafin Corona ba &#8211; Gwamatin Jahar Edo &#160; Gwamnatin jahar Edo ta bayyana cewa dole ne maazauna jahar su yi riga-kafin corona ko kuma ta bullo musu ta bayan gida. Gwamnan jahar, Godwin Obaseki ya ce za a hana shiga masallatai, majami&#8217;u da bankuna ba tare da [&#8230;]</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/tsauraran-matakai-rigakafin-corona/" data-wpel-link="internal">Zamu Saka Tsauraran Matakai Kan Wanda Basu yi Rigakafin Corona ba &#8211; Gwamatin Jahar Edo</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></description>
										<content:encoded><![CDATA[<p><strong>Zamu Saka Tsauraran Matakai Kan Wanda Basu yi Rigakafin Corona ba &#8211; Gwamatin Jahar Edo</strong></p>
<p>&nbsp;</p>
<p>Gwamnatin jahar Edo ta bayyana cewa dole ne maazauna jahar su yi riga-kafin corona ko kuma ta bullo musu ta bayan gida.</p>
<p>Gwamnan jahar, Godwin Obaseki ya ce za a hana shiga masallatai, majami&#8217;u da bankuna ba tare da shaidar yin riga-kafin ba.</p>
<p>Kamar yadda ya shaida, tarukan shagulgulan biki za su haramta ga duk wanda bashi da shaidar yin riga-kafin muguwar cutar.</p>
<p>Benin City, Edo &#8211; Gwamnatin jahar Edo ta ce za ta saka tsauraran matakai a bankuna, majami&#8217;u, masallatai da wuraren shagulgulan biki kan duk wanda bai nuna shaidar yin riga-kafin cutar korona ba daga watan Satumba.</p>
<p>Daily Trust ta rawaito cewa, Gwamna Godwin Obaseki na jahar ya sanar da hakan ranar Litinin yayin kaddamar da kashi biyu na riga-kafin cutar corona a Benin City.</p>
<p>Bayanin Obaseki kan matakin da zai dauka Ya ce cutar korona nau&#8217;in Delta na yaduwa sosai kuma tana cigaba da yaduwa a kowanne lokaci, lamarin da yasa dole jama&#8217;a su yi riga-kafin cutar, Daily Trust ta rawaito.</p>
<p>Muna da nau&#8217;ikan riga-kafi biyu, akwai riga-kafin Moderna wanda bamu dade da samu ba, akwai kuma riga-kafin Astrazeneca ga wadanda z asu karba kashi na biyunsu.</p>
<p>A cikin kwanakin karshen makon nan ne jahar Edo ta karba magugunan allurar riga-kafi 76,712, wanda ya hada da allurai 65,016 na Moderna da 11,696 na AstraZeneca.</p>
<p>Kamar yadda yace, gwamnati ba za ta rufe jahar ba amma za ta baiwa rayukan jama&#8217;a kariya. Ya kara da cewa daga watan Satumba, za a haramta shiga taro mai mutane da yawa ga wadanda basu karba riga-kafin cutar ba.</p>
<p>Daga mako na biyu na watan Satumba, ba za a bar jama&#8217;a su shiga majami&#8217;u, masallatai, wuraren shagulgulan biki, liyafofi da kuma wuraren cin abinci ba, ba tare da katin shaidar yin riga-kafin ba.</p>
<p>Hakazalika, daga mako na biyu na watan Satumba, ba za a bar jama&#8217;a su dinga shiga bankuna ba, ba tare da katin shaidar yin riga-kafin cutar corona ba. Don haka duk wanda yake son walwala, yayi riga-kafi kawai.</p>
<p>&nbsp;</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/tsauraran-matakai-rigakafin-corona/" data-wpel-link="internal">Zamu Saka Tsauraran Matakai Kan Wanda Basu yi Rigakafin Corona ba &#8211; Gwamatin Jahar Edo</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></content:encoded>
					
					<wfw:commentRss>https://hausa.arewaagenda.com/tsauraran-matakai-rigakafin-corona/feed/</wfw:commentRss>
			<slash:comments>0</slash:comments>
		
		
		<post-id xmlns="com-wordpress:feed-additions:1">6817</post-id>	</item>
		<item>
		<title>Matsalar Tsaro: Gwamnonin PDP 13 Sun Shiga Ganawa</title>
		<link>https://hausa.arewaagenda.com/matsalar-tsaro-gwamnonin-ganawa/</link>
					<comments>https://hausa.arewaagenda.com/matsalar-tsaro-gwamnonin-ganawa/#respond</comments>
		
		<dc:creator><![CDATA[Khadija Garba]]></dc:creator>
		<pubDate>Mon, 17 May 2021 21:49:54 +0000</pubDate>
				<category><![CDATA[SIYASA]]></category>
		<category><![CDATA[Abia]]></category>
		<category><![CDATA[adamawa]]></category>
		<category><![CDATA[Akwa Ibom]]></category>
		<category><![CDATA[Aminu tambuwal]]></category>
		<category><![CDATA[bala mohammed]]></category>
		<category><![CDATA[bauchi]]></category>
		<category><![CDATA[bayelsa]]></category>
		<category><![CDATA[benue]]></category>
		<category><![CDATA[Delta]]></category>
		<category><![CDATA[Douye Diri]]></category>
		<category><![CDATA[Edo]]></category>
		<category><![CDATA[Emmanuel Udom]]></category>
		<category><![CDATA[enugu]]></category>
		<category><![CDATA[Godwin Obaseki]]></category>
		<category><![CDATA[Ifeanyi Okowa]]></category>
		<category><![CDATA[Ifeanyi Ugwuanyi]]></category>
		<category><![CDATA[Matsalar Tsaro]]></category>
		<category><![CDATA[Nyesom Wike]]></category>
		<category><![CDATA[Okezie Ikpeazu]]></category>
		<category><![CDATA[PDP]]></category>
		<category><![CDATA[Ribas]]></category>
		<category><![CDATA[Sakkwato]]></category>
		<category><![CDATA[samuel ortom]]></category>
		<category><![CDATA[umar fintiri]]></category>
		<guid isPermaLink="false">https://arewaagenda.com/hausa/?p=5173</guid>

					<description><![CDATA[<p>Matsalar Tsaro: Gwamnonin PDP 13 Sun Shiga Ganawa &#160; Wasu gwamnoni a karkashin inuwar jam&#8217;iyyar PDP sun shiga tattaunawar sirri kan batun tsaro. Gwamnonin 13 suna ganawa ne a jahar Oyo, inda ake sa ran isowar wasu sauran gwamnonin. Ana sa ran za su tattauna kan batun rashin tsaron Najeriya da kuma ci gaban jam&#8217;iyyarsu [&#8230;]</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/matsalar-tsaro-gwamnonin-ganawa/" data-wpel-link="internal">Matsalar Tsaro: Gwamnonin PDP 13 Sun Shiga Ganawa</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></description>
										<content:encoded><![CDATA[<p><strong>Matsalar Tsaro: Gwamnonin PDP 13 Sun Shiga Ganawa</strong></p>
<p>&nbsp;</p>
<p>Wasu gwamnoni a karkashin inuwar jam&#8217;iyyar PDP sun shiga tattaunawar sirri kan batun tsaro.</p>
<p>Gwamnonin 13 suna ganawa ne a jahar Oyo, inda ake sa ran isowar wasu sauran gwamnonin.</p>
<p>Ana sa ran za su tattauna kan batun rashin tsaron Najeriya da kuma ci gaban jam&#8217;iyyarsu ta PDP.</p>
<p>Gwamnonin jahohi 13 a karkashin jam&#8217;iyyar PDP, a yanzu haka suna ganawa a Cibiyar Taron Kasa da Kasa na Cibiyar Kula da Noma ta IITA dake Ibadan ranar Litinin, Daily Nigerian ta ruwaito.</p>
<p>Gwamnonin su ne:</p>
<p>Aminu Tambuwal na jahar Sakkwato; Samuel Ortom na Benue; Douye Diri na Bayelsa; Okezie Ikpeazu na Abia da Emmanuel Udom na Akwa Ibom.</p>
<p>Sauran sune:</p>
<p>Ifeanyi Okowa na Delta, Ifeanyi Ugwuanyi na jahar Enugu, Umar Fintiri na Adamawa; Bala Mohammed na jahar Bauchi, Nyesom Wike na Ribas da Godwin Obaseki na Edo. Akwai kuma gwamna mai masaukin baki, Seyi Makinde na Jahar Oyo da Mataimakin Gwamnan Zamfara, Aliyu Gusau wanda ya wakilci Gwamna Bello Matawalle.</p>
<p>Ana sa ran Gwamna Darius Ishaku, na Taraba da Gwamna Ben Ayade, na Kuros Riba za su shigo yayin da taron ke ci gaba. Gwamnonin da suka iso cibiyar taron daidai karfe 1:10 na rana a cikin motar bas sun shiga ganawar sirri.</p>
<p>NAN ta tattaro daga wurin taron cewa taron zai mayar da hankali ne kan yanayin tsaro a kasar.</p>
<p>Ta kuma tattaro cewa taron wanda Shugaban gamayyar gwamnonin PDP ya jagoranta, Gwamna Aminu Tambuwal zai tattauna wasu batutuwan da suka shafi ci gaban jam&#8217;iyyar.</p>
<p>Ana sa ran za a fitar da sanarwa bayan taro.</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/matsalar-tsaro-gwamnonin-ganawa/" data-wpel-link="internal">Matsalar Tsaro: Gwamnonin PDP 13 Sun Shiga Ganawa</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></content:encoded>
					
					<wfw:commentRss>https://hausa.arewaagenda.com/matsalar-tsaro-gwamnonin-ganawa/feed/</wfw:commentRss>
			<slash:comments>0</slash:comments>
		
		
		<post-id xmlns="com-wordpress:feed-additions:1">5173</post-id>	</item>
		<item>
		<title>Jam&#8217;iyyar APC ta Bukaci Wani Gwamna da ya yi Murabus</title>
		<link>https://hausa.arewaagenda.com/apc-bukaci-gwamna-murabus/</link>
					<comments>https://hausa.arewaagenda.com/apc-bukaci-gwamna-murabus/#respond</comments>
		
		<dc:creator><![CDATA[Khadija Garba]]></dc:creator>
		<pubDate>Mon, 21 Dec 2020 11:14:40 +0000</pubDate>
				<category><![CDATA[SIYASA]]></category>
		<category><![CDATA[APC]]></category>
		<category><![CDATA[Edo]]></category>
		<category><![CDATA[Godwin Obaseki]]></category>
		<guid isPermaLink="false">https://arewaagenda.com/hausa/?p=2999</guid>

					<description><![CDATA[<p>Jam&#8217;iyyar APC ta Bukaci Wani Gwamna da ya yi Murabus Jam’iyyar APC ta zargi Gwamna Godwin Obaseki da rashin iya mulki. Shugaban APC, ya bukaci Gwamnan jihar ya rubuta takardar murabus. APC ta zargi Obaseki da laftowa Gwamnatin Edo bashi da rashin tsaro Shugaban jam’iyyar APC na rikon kwarya a jihar Edo, Kanal David Imuse, [&#8230;]</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/apc-bukaci-gwamna-murabus/" data-wpel-link="internal">Jam&#8217;iyyar APC ta Bukaci Wani Gwamna da ya yi Murabus</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></description>
										<content:encoded><![CDATA[<p><strong>Jam&#8217;iyyar APC ta Bukaci Wani Gwamna da ya yi Murabus</strong></p>
<p>Jam’iyyar APC ta zargi Gwamna Godwin Obaseki da rashin iya mulki.</p>
<p>Shugaban APC, ya bukaci Gwamnan jihar ya rubuta takardar murabus.</p>
<p>APC ta zargi Obaseki da laftowa Gwamnatin Edo bashi da rashin tsaro Shugaban jam’iyyar APC na rikon kwarya a jihar Edo, Kanal David Imuse, ya fito ya yi kaca-kaca da salon mulkin gwamna Godwin Obaseki.</p>
<p>Jaridar Vanguard ta fitar da rahoto cewa David Imuse ya bukaci Mai girma gwamna Godwin Obaseki ya yi murabus, ya bar wa wani kujerar.</p>
<p>A ranar Lahadi, 20 ga watan Disamba, 2020, Kanal Imuse ya yi wannan kira, ya ce Godwin Obaseki bai san abin da yake yi a ofishin gwamna ba.</p>
<p>A cewar shugaban jam’iyyar hamayyar ta APC, dabaru sun karewa gwamnatin Obaseki a jihar Edo.</p>
<p>Ganin yadda bashin da ke kan gwamnatin Edo ya ke kara taruwa, jam’iyyar APC ta na ganin babu abin da ya fi irin Mista Obaseki ya ajiye mulki.</p>
<p>Bayan haka, jam’iyyar APC mai adawa a Edo, ta na kukan halin rashin tsaro da ake fama da shi, tare da zargin gwamnatin Obaseki da saba doka.</p>
<p>Hakan na zuwa ne a lokacin da ake yawan samun sace-sace da tashin-tashina tun da aka samu wasu marasa gaskiya da su ka tsere daga kurkuku.</p>
<p>Jaridar Premium Times ta yi yunkurin jin ta-bakin gwamnan bayan kiran da David Imuse ya yi, amma Godwin Obaseki bai amsa kiran wayarsa ba.</p>
<p>Tuni shugaban PDP na Edo, Chris Nehikhare ya yi wa takwaransa na jam’iyyar APC raddi, ya ce bai kamata ya rika yin irin wadannan kalamai ba.</p>
<p>Kwanki gwamna Godwin Obaseki ya yi wa tsohon Mai gidansa, Adams Oshiomhole gorin kudi.</p>
<p>Abin har ta kai Godwin Obaseki ya na bada labarin yadda su ka taimakawa Oshiomhole ya nemi kujerar gwamnan jihar Edo karkashin jam&#8217;iyyar AC.</p>
<p>Obaseki ya bayyana rawar da ya taka a kotu har aka karbe nasarar Oserheimen Osunbor da jam&#8217;iyyar PDP, aka ba Oshiomhole nasara a zaben Edo.</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/apc-bukaci-gwamna-murabus/" data-wpel-link="internal">Jam&#8217;iyyar APC ta Bukaci Wani Gwamna da ya yi Murabus</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></content:encoded>
					
					<wfw:commentRss>https://hausa.arewaagenda.com/apc-bukaci-gwamna-murabus/feed/</wfw:commentRss>
			<slash:comments>0</slash:comments>
		
		
		<post-id xmlns="com-wordpress:feed-additions:1">2999</post-id>	</item>
	</channel>
</rss>

<!--
Performance optimized by W3 Total Cache. Learn more: https://www.boldgrid.com/w3-total-cache/?utm_source=w3tc&utm_medium=footer_comment&utm_campaign=free_plugin

Page Caching using Disk: Enhanced 

Served from: hausa.arewaagenda.com @ 2026-07-11 18:25:15 by W3 Total Cache
-->