<?xml version="1.0" encoding="UTF-8"?><rss version="2.0"
	xmlns:content="http://purl.org/rss/1.0/modules/content/"
	xmlns:wfw="http://wellformedweb.org/CommentAPI/"
	xmlns:dc="http://purl.org/dc/elements/1.1/"
	xmlns:atom="http://www.w3.org/2005/Atom"
	xmlns:sy="http://purl.org/rss/1.0/modules/syndication/"
	xmlns:slash="http://purl.org/rss/1.0/modules/slash/"
	>

<channel>
	<title>Delta Archives - Arewa Agenda Hausa</title>
	<atom:link href="https://hausa.arewaagenda.com/tag/delta/feed/" rel="self" type="application/rss+xml" />
	<link>https://hausa.arewaagenda.com/tag/delta/</link>
	<description>Arewa Labarai Hausa</description>
	<lastBuildDate>Sun, 17 Mar 2024 10:28:04 +0000</lastBuildDate>
	<language>en-US</language>
	<sy:updatePeriod>
	hourly	</sy:updatePeriod>
	<sy:updateFrequency>
	1	</sy:updateFrequency>
	<generator>https://wordpress.org/?v=6.9.4</generator>
	<atom:link rel='hub' href='https://hausa.arewaagenda.com/?pushpress=hub'/>
<site xmlns="com-wordpress:feed-additions:1">229835694</site>	<item>
		<title>&#8216;Yan Bindiga Sun Hallaka Manyan Jami&#8217;an Sojoji 22 a Jihar Delta</title>
		<link>https://hausa.arewaagenda.com/yanbindiga-halaka-sojoji-delta/?utm_source=rss&#038;utm_medium=rss&#038;utm_campaign=yanbindiga-halaka-sojoji-delta</link>
					<comments>https://hausa.arewaagenda.com/yanbindiga-halaka-sojoji-delta/#respond</comments>
		
		<dc:creator><![CDATA[Khadija Garba]]></dc:creator>
		<pubDate>Sun, 17 Mar 2024 10:28:04 +0000</pubDate>
				<category><![CDATA[Taska]]></category>
		<category><![CDATA['yan bindiga]]></category>
		<category><![CDATA[Delta]]></category>
		<category><![CDATA[Janar Chirstopher Gwabin Musa]]></category>
		<category><![CDATA[Laftanar Kanal]]></category>
		<category><![CDATA[Sojojin]]></category>
		<guid isPermaLink="false">https://hausa.arewaagenda.com/?p=14162</guid>

					<description><![CDATA[<p>&#8216;Yan Bindiga Sun Hallaka Manyan Jami&#8217;an Sojoji 22 a Jihar Delta &#160; Wasu ƴan bindiga sun yi wa sojoji kwanton ɓauna a ƙauyen Okuoma da ke ƙaramar hukumar Ughelli ta Kudu a jihar Delta, inda suka kashe da dama daga cikinsu. Rundunar soji ta tabbatar da faruwar lamarin a ranar Asabar, inda ta sha alwashin [&#8230;]</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/yanbindiga-halaka-sojoji-delta/" data-wpel-link="internal">&#8216;Yan Bindiga Sun Hallaka Manyan Jami&#8217;an Sojoji 22 a Jihar Delta</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></description>
										<content:encoded><![CDATA[<p><strong>&#8216;Yan Bindiga Sun Hallaka Manyan Jami&#8217;an Sojoji 22 a Jihar Delta</strong></p>
<p>&nbsp;</p>
<p>Wasu ƴan bindiga sun yi wa sojoji kwanton ɓauna a ƙauyen Okuoma da ke ƙaramar hukumar Ughelli ta Kudu a jihar Delta, inda suka kashe da dama daga cikinsu.</p>
<p>Rundunar soji ta tabbatar da faruwar lamarin a ranar Asabar, inda ta sha alwashin bin diddigin wasu matasa, waɗanda suka farmaki sojojin.</p>
<p>Daraktan yaɗa labarai na tsaro, Tukur Gusau, ya ce wasu matasa ne a ƙaramar hukumar Bomadi ta jihar ɗauke da makamai suka farmaki sojojin tare da halaka su.</p>
<p>Asaba, jihar Delta &#8211; Aƙalla sojoji 22 ne wasu ƴan bindiga a ƙauyen Okuoma suka halaka a ƙaramar hukumar Ughelli ta Kudu a jihar Delta.</p>
<p>Jaridar The Nation ta ruwaito cewa sojojin na Bataliya ta 181, Bomadi, sun je aikin ceto ne a lokacin da maharan suka yi musu kwanton ɓauna a ranar Alhamis 14 ga watan Maris.</p>
<p>Jaridar Daily Trust ta ce lamarin ya fara ne a ranar Alhamis lokacin da sojojin suka samu kiran gaggawa kan rikicin ƙabilanci da ya ɓarke tsakanin mutanen ƙauyukan Okuoma da Okoloba.</p>
<p>Yadda aka yi wa sojojin kwanton ɓauna</p>
<p>Sun je aikin ceto ne a ƙauyen Okuoma domin kuɓutar da wani matashi, Mista Anthony Aboh, na ƙauyen Okoloba a ƙaramar hukumar Bomadi wanda aka sace saboda rikicin filin da ake yi tsakanin ƙauyukan.</p>
<p>Wani majiya ya ce an mamayi sojojin ne lokacin da suke dawowa bayan sun gama tattaunawar da bata haifar da ɗa mai ido ba kan matashin a ɗakin taro na ƙauyen Okuoma.</p>
<p>&#8220;Mutane da dama aka halaka da suka haɗa da wani tsohon ɗan majalisa daga ƙauyen Okoloba wanda ya kai rahoton lamarin ga JTF.</p>
<p>&#8220;Amma, kwamandan da sauran sojojin an yi garkuwa da su ne, inda aka kai su wani ɓoyayyen waje kusa da ƙauyen da ke makwabtaka.</p>
<p>Sojojin da aka kashe</p>
<p>Majiyar ya ƙara da cewa an tabbatar da halaka sojoji 22 a ƙauyen Okuoma.<br />
Daga cikinsu akwai Laftanar Kanal ɗaya, Manjo biyu, Kyaftin ɗaya da sojoji 18.</p>
<p>Wasu daga cikin sojojin da aka kashe sun haɗa da Manjo Shafa, Manjo Obi, Kyaftin Zakari da Laftanar Kanal A. H. Ali.</p>
<p>Babban hafsan hafsoshin tsaro (CDS), Janar Christopher Gwabin Musa ya bayar da umarnin gudanar da bincike cikin gaggawa tare da cafke wadanda ke da hannu a wannan ɗanyen aikin.</p>
<p>A wata sanarwa da muƙaddashin daraktan yaɗa labarai na tsaro, Birgediya Janar Tukur Gusau, ya fitar a ranar Asabar, ya bayyana hakan, inda ya ƙara da cewa an kai rahoton lamarin ga gwamnatin jihar Delta.</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/yanbindiga-halaka-sojoji-delta/" data-wpel-link="internal">&#8216;Yan Bindiga Sun Hallaka Manyan Jami&#8217;an Sojoji 22 a Jihar Delta</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></content:encoded>
					
					<wfw:commentRss>https://hausa.arewaagenda.com/yanbindiga-halaka-sojoji-delta/feed/</wfw:commentRss>
			<slash:comments>0</slash:comments>
		
		
		<post-id xmlns="com-wordpress:feed-additions:1">14162</post-id>	</item>
		<item>
		<title>Gini Mai Hawa 20 ya Ruguje Kan Jama&#8217;a a Jihar Delta</title>
		<link>https://hausa.arewaagenda.com/gini-ruguje-jamaa-delta/?utm_source=rss&#038;utm_medium=rss&#038;utm_campaign=gini-ruguje-jamaa-delta</link>
		
		<dc:creator><![CDATA[Khadija Garba]]></dc:creator>
		<pubDate>Fri, 15 Sep 2023 13:03:46 +0000</pubDate>
				<category><![CDATA[Taska]]></category>
		<category><![CDATA[Delta]]></category>
		<category><![CDATA[Rugujewar Gini]]></category>
		<guid isPermaLink="false">https://hausa.arewaagenda.com/?p=13741</guid>

					<description><![CDATA[<p>Gini Mai Hawa 20 ya Ruguje Kan Jama&#8217;a a Jihar Delta &#160; Mutane da dama sun samu raunuka yayin da wani gini mai hawa 20 ya kife a Asaba jihar Delta da yammacin Alhamis. Ganau sun bayyana cewa lamarin ya faru ba zato ba tsammani yayin da ma&#8217;aikata ke ci gaba da aikin ginin. Kwamishininan [&#8230;]</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/gini-ruguje-jamaa-delta/" data-wpel-link="internal">Gini Mai Hawa 20 ya Ruguje Kan Jama&#8217;a a Jihar Delta</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></description>
										<content:encoded><![CDATA[<p><strong>Gini Mai Hawa 20 ya Ruguje Kan Jama&#8217;a a Jihar Delta</strong></p>
<p>&nbsp;</p>
<p>Mutane da dama sun samu raunuka yayin da wani gini mai hawa 20 ya kife a Asaba jihar Delta da yammacin Alhamis.</p>
<p>Ganau sun bayyana cewa lamarin ya faru ba zato ba tsammani yayin da ma&#8217;aikata ke ci gaba da aikin ginin.</p>
<p>Kwamishininan sabunta birane na gwamnatin jihar Delta ya ce sun fara gudanar da bincike don gano ainihin abinda ya faru.</p>
<p>Delta &#8211; Wani ginin bene mai hawa 20 da ake aikin ginawa ya ruguje a Asaba, babban birnin jihar Delta, kamar yadda jaridar Leadership ta ruwaito.</p>
<p>A cewar wani ganau da ibtila&#8217;in ya auku a kan idonsa, lamarin ya yi sanadin raunata mutane kusan takwas ranar Alhamis, 14 ga watan Satumba,2023.</p>
<p>Ginin otal ɗin na biliyoyin Naira da ke daura da Delta Mall ya ruguje ne da yammacin ranar Alhamis yayin da ma&#8217;aikata ke tsaka da aiki.</p>
<p>An tattaro cewa ginin otal ɗin mallakin hamshakin attajirin dan kasuwa ne kuma wanda ya kafa kamfanin RainOil Group, Cif Gabriel Ogbechie.</p>
<p>Jami’an hukumar bada agajin gaggawa ta jihar Delta da jami’an tsaro sun kewaye wurin da lamarin ya faru a halin yanzu, kamar yadda Channels tv ta rahoto.</p>
<p>Mutun nawa rushewar ginin ta shafa?</p>
<p>Wata shaidar gani da ido ta ce ita da wasu da ke kasuwanci a kusa da wurin sun yi mamakin yadda kwatsam suka ji kara yayin da ma’aikatan ke tsaka da aikin ginin.</p>
<p>Matar, wacce ta bayyana sunanta da, Onyinye Okei, ta ce kusan ma&#8217;aikata Takwas suka samu raunuka kuma tuni abokan aikinsu suka garzaya da su Asibiti.</p>
<p>Me ya haddasa rugujewar ginin?</p>
<p>Da yake zantawa da manema labarai bayan kammala duba ginin da ya ruguje, kwamishinan sabunta biranen jihar, Mista Michael Anoka, ya ce lamarin ya faru ne sakamakon rashin ingancin ginin.</p>
<p>Anoka, wanda ya tabbatar babu wanda ya mutu, ya ce:</p>
<p>&#8220;Muna kan aikin bincike don gano musabbabin faruwar lamarin kuma gwamnati ta fara daukar matakai kamar yadda kuke gani an rufe wurin. Bayan mun gama bincike, zamu faɗi rahoton abinda muka gano.&#8221;</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/gini-ruguje-jamaa-delta/" data-wpel-link="internal">Gini Mai Hawa 20 ya Ruguje Kan Jama&#8217;a a Jihar Delta</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></content:encoded>
					
		
		
		<post-id xmlns="com-wordpress:feed-additions:1">13741</post-id>	</item>
		<item>
		<title>Kungiyar Matasan Warri ta Yanke Hukuncin Bulala 40 ko Tarar N10,000 ga Mata Masu Shigar Banza</title>
		<link>https://hausa.arewaagenda.com/bulala-tara-shigar-banza/?utm_source=rss&#038;utm_medium=rss&#038;utm_campaign=bulala-tara-shigar-banza</link>
					<comments>https://hausa.arewaagenda.com/bulala-tara-shigar-banza/#respond</comments>
		
		<dc:creator><![CDATA[Khadija Garba]]></dc:creator>
		<pubDate>Sat, 15 Jul 2023 13:57:18 +0000</pubDate>
				<category><![CDATA[Taska]]></category>
		<category><![CDATA[Delta]]></category>
		<category><![CDATA[Shigar Banza]]></category>
		<guid isPermaLink="false">https://hausa.arewaagenda.com/?p=13473</guid>

					<description><![CDATA[<p>Kungiyar Matasan Warri ta Yanke Hukuncin Bulala 40 ko Tarar N10,000 ga Mata Masu Shigar Banza &#160; &#160; Matasan yankin karamar hukumar Warri ta kudu a jihar Delta sun ɗauri damarar yaƙar shigar rashin ɗa&#8217;a da yan mata ke yi. Ƙungiyar matasan ta yanke hukuncin Bulala 40 ko tarar N10,000 ga duk macen da aka [&#8230;]</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/bulala-tara-shigar-banza/" data-wpel-link="internal">Kungiyar Matasan Warri ta Yanke Hukuncin Bulala 40 ko Tarar N10,000 ga Mata Masu Shigar Banza</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></description>
										<content:encoded><![CDATA[<p><strong>Kungiyar Matasan Warri ta Yanke Hukuncin Bulala 40 ko Tarar N10,000 ga Mata Masu Shigar Banza</strong></p>
<p>&nbsp;</p>
<p>&nbsp;</p>
<p>Matasan yankin karamar hukumar Warri ta kudu a jihar Delta sun ɗauri damarar yaƙar shigar rashin ɗa&#8217;a da yan mata ke yi.</p>
<p>Ƙungiyar matasan ta yanke hukuncin Bulala 40 ko tarar N10,000 ga duk macen da aka kama ta yi shigar nuna tsiraici.</p>
<p>Sun ce ba zasu lamurci yanayin shigar da &#8216;yan matan ke yi da sunan wayewa ba, dole su koya nusu tarbiyya.</p>
<p>Delta State &#8211; Ƙungiyar matasa mai suna &#8216;Ubeji Youth and Employment Development&#8217; da ke ƙaramar hukumar Warri ta kudu a jihar Delta sun ɗauki matakin gyara tarbiyya a yankinsu.</p>
<p>Ƙungiyar ta cimma matsaya kuma ta amince da hukuncin bulala 40 ga kowace matashiyar budurwa da aka kama ta yi shigar rashin ɗa&#8217;a ta jan hankali a garinsu.</p>
<p>Jaridai Daily Trust ta ranar Asabar ta tattaro rahoton cewa ƙungiyar ta kuma bada zaɓin tarar N10,000 ga duk macen da aka kama da saɓa wa dokar shigar banza a yankin.</p>
<p>Sakataren ƙungiyar matasan, Mista Stanley Bomele, shi ne ya bayyana haka yayin da yake hira da manema labarai a jihar Delta.</p>
<p>Ya ƙara da cewa matasa sun yanke fara aiki mai taken, &#8220;Yaƙi da shigar banza,&#8221; a tsakanin matasan &#8216;yan mata a yankin, wanda ke neman zama ruwan dare.</p>
<p>Mista Bemele ya ce wannan matakin ya zama wajibi sakamakon yadda shigar mata ke ƙara lalacewa kullum, sun koma sanya kaya na rashin ɗa&#8217;a da rashin tarbiyya a yankin.</p>
<p>An haramta wa mata sa matsattsun kaya?</p>
<p>Bugu da ƙari, Sakataren ya sanar da cewa daga ranar, sun ta haramta wa mata sanya ƙananan Siket (Minisikets) da sauran matsattsun kaya da ke fito da surar jikinsu.</p>
<p>Ya yi gargaɗin cewa ba zasu lamurci ganin &#8216;yan mata na sanya irin waɗan nan kayan ba saboda su ne babbar ƙofar da ke haddasa yawaitar lalata da cin zarafin mata.</p>
<p>Ya ce yanzun da yawan matan yankin sun lalace wajen sanya kaya da sunan wayewa, da yawansu suna fitowa tamkar tsirara, kamar yadda Punch ta ruwaito.</p>
<p>Ya ce wannan aikin na hukunta duk wacce ta yi shigar banza zai ci gaba daga nan har zuwa lokacin da matan yankin zasu shiga taitayinsu, su riƙa shiga ta kamala.</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/bulala-tara-shigar-banza/" data-wpel-link="internal">Kungiyar Matasan Warri ta Yanke Hukuncin Bulala 40 ko Tarar N10,000 ga Mata Masu Shigar Banza</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></content:encoded>
					
					<wfw:commentRss>https://hausa.arewaagenda.com/bulala-tara-shigar-banza/feed/</wfw:commentRss>
			<slash:comments>0</slash:comments>
		
		
		<post-id xmlns="com-wordpress:feed-additions:1">13473</post-id>	</item>
		<item>
		<title>Hukumar INEC ta Tabbatar da Sace Na&#8217;urar BVAS a Jihar Katsina da Delta</title>
		<link>https://hausa.arewaagenda.com/sace-bvas-katsina-delta/?utm_source=rss&#038;utm_medium=rss&#038;utm_campaign=sace-bvas-katsina-delta</link>
					<comments>https://hausa.arewaagenda.com/sace-bvas-katsina-delta/#respond</comments>
		
		<dc:creator><![CDATA[Khadija Garba]]></dc:creator>
		<pubDate>Sat, 25 Feb 2023 15:09:08 +0000</pubDate>
				<category><![CDATA[Taska]]></category>
		<category><![CDATA[BVAS]]></category>
		<category><![CDATA[Delta]]></category>
		<category><![CDATA[INEC]]></category>
		<category><![CDATA[katsina]]></category>
		<guid isPermaLink="false">https://hausa.arewaagenda.com/?p=12721</guid>

					<description><![CDATA[<p>Hukumar INEC ta Tabbatar da Sace Na&#8217;urar BVAS a Jihar Katsina da Delta &#160; &#160; Hukumar zabe mai zaman kanta ta bayyana cewa, a yanzu babban abin da &#8216;yan daba suka mai da hankali akai shine na&#8217;urar BVAS. An farmaki rumfunan zabe a jihohin Katsina da Delta a zaben yau Asabar 25 ga watan Faburairu. [&#8230;]</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/sace-bvas-katsina-delta/" data-wpel-link="internal">Hukumar INEC ta Tabbatar da Sace Na&#8217;urar BVAS a Jihar Katsina da Delta</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></description>
										<content:encoded><![CDATA[<p><strong>Hukumar INEC ta Tabbatar da Sace Na&#8217;urar BVAS a Jihar Katsina da Delta</strong></p>
<p>&nbsp;</p>
<p>&nbsp;</p>
<p>Hukumar zabe mai zaman kanta ta bayyana cewa, a yanzu babban abin da &#8216;yan daba suka mai da hankali akai shine na&#8217;urar BVAS.</p>
<p>An farmaki rumfunan zabe a jihohin Katsina da Delta a zaben yau Asabar 25 ga watan Faburairu.</p>
<p>A wasu rumfunan a Najeriya, ana ci gaba da kada kuri&#8217;u kana babu wani tashin hankali da ake fuskanta.</p>
<p>FCT, Abuja &#8211; Hukumar zabe mai zaman kanta (INEC) ta bayyana cewa, wasu &#8216;yan daba sun yi awon gaba da na&#8217;urar tantance masu kada kuri&#8217;u ta BVAS da jihohin Katsina da Delta.</p>
<p>Mahmud Yakubu, shugaban INEC ne ya bayyana hakan yayin da yake zantawa da manema labarai a cibiyar tattara sakamakon zabe da ke Abuja kan halin da ake ciki a zaben shugaban kasa da &#8216;yan majalisun tarayya.</p>
<p>Yakubu ya shaida cewa, duba da yadda zaben ke gudana a kasar, alamu sun nuna akwai kalubalen da ba a rasa ba, TheCable ta ruwaito.</p>
<p>Ya ce, kalubalen da ake fuskanta sun hada da matsalar jigilar kayan aikin zaben da kuma rashin tsaro.</p>
<p>Jaridar The Nation ta ruwaito cewa, tuni hukumar ta zabe ta tabbatar da maye gurbin na&#8217;urorin da aka sacen don ci gaba da zabe a yankunan.</p>
<p>A ina lamarin ya faru?</p>
<p>A cewar shugaban na INEC, an sace wasu na&#8217;urorin ne a karamar Safana ta jihar Katsina a Arewa maso Yammacin Najeriya.</p>
<p>A gefen Kudancin kasar nan kuwa, an sace na&#8217;urorin na BVAS ne a karamar hukumar Oshimili ta jihar Delta.</p>
<p>Da yake bayyana matakin da aka dauka, shugaban ya ce an maye gurbin na&#8217;urorin yayin da &#8216;yan sanda suka kwato uku daga cikin shida na na&#8217;urorin da aka sace a jihar Katsina.</p>
<p>A cewarsa:</p>
<p>&#8220;Wannan karon, BVAS ne babban abin harin &#8216;yan daba ba wai akwatunan zabe ba da aka sani a baya.&#8221;</p>
<p>&nbsp;</p>
<p>&nbsp;</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/sace-bvas-katsina-delta/" data-wpel-link="internal">Hukumar INEC ta Tabbatar da Sace Na&#8217;urar BVAS a Jihar Katsina da Delta</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></content:encoded>
					
					<wfw:commentRss>https://hausa.arewaagenda.com/sace-bvas-katsina-delta/feed/</wfw:commentRss>
			<slash:comments>0</slash:comments>
		
		
		<post-id xmlns="com-wordpress:feed-additions:1">12721</post-id>	</item>
		<item>
		<title>Sunayen Kwamishinoni 53 da Suka yi Murabus Daga Mukamansu a Jahohi 7</title>
		<link>https://hausa.arewaagenda.com/sunayen-kwamishinoni-suka/?utm_source=rss&#038;utm_medium=rss&#038;utm_campaign=sunayen-kwamishinoni-suka</link>
					<comments>https://hausa.arewaagenda.com/sunayen-kwamishinoni-suka/#respond</comments>
		
		<dc:creator><![CDATA[Khadija Garba]]></dc:creator>
		<pubDate>Tue, 19 Apr 2022 14:03:20 +0000</pubDate>
				<category><![CDATA[SIYASA]]></category>
		<category><![CDATA[Akwa Ibom]]></category>
		<category><![CDATA[benue]]></category>
		<category><![CDATA[Delta]]></category>
		<category><![CDATA[Hadimai]]></category>
		<category><![CDATA[kaduna]]></category>
		<category><![CDATA[Kano]]></category>
		<category><![CDATA[Kwamishinoni]]></category>
		<category><![CDATA[kwara]]></category>
		<category><![CDATA[Rivers]]></category>
		<guid isPermaLink="false">https://hausa.arewaagenda.com/?p=10193</guid>

					<description><![CDATA[<p>Sunayen Kwamishinoni 53 da Suka yi Murabus Daga Mukamansu a Jahohi 7 Kamar yadda tanadin sashi na 84, sakin layi na 12 ya tanadar na gyararrun dokokin zabe, a kalla kwamishinoni 53 da wasu hadiman gwamnonin jiha ne suka yi murabus daga mukamansu domin neman kujerun siyasa kafin zuwan zaben 2023. Wannan na zuwa ne [&#8230;]</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/sunayen-kwamishinoni-suka/" data-wpel-link="internal">Sunayen Kwamishinoni 53 da Suka yi Murabus Daga Mukamansu a Jahohi 7</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></description>
										<content:encoded><![CDATA[<p><strong>Sunayen Kwamishinoni 53 da Suka yi Murabus Daga Mukamansu a Jahohi 7</strong></p>
<p>Kamar yadda tanadin sashi na 84, sakin layi na 12 ya tanadar na gyararrun dokokin zabe, a kalla kwamishinoni 53 da wasu hadiman gwamnonin jiha ne suka yi murabus daga mukamansu domin neman kujerun siyasa kafin zuwan zaben 2023.</p>
<p>Wannan na zuwa ne bayan ministoci a matakin tarayya da suka hada da Rotimi Amaechi, Sanata Chris Ngige, Abubakar Malami da wasu shugabannin cibiyoyin tarayya da ke hango kujerun siyasa suka yi mirsisi suka ki murabus.</p>
<p>Yayin da Amaechi tuntuni ya bayyana burinsa na gaje Buhari, Malami kamar yadda majiyoyi makusantansa suka sanar, zai nemi kujerar gwamnan jiharsa. Daily Trust ta ruwaito cewa, shugabannin cibiyoyin tarayya da ke hararo kujerun gwamna, Sanata da &#8216;yan majalisun tarayya suna da yawa.</p>
<p>Darakta janar na NIMASA, Bashir Yusuf Jamoh, a kwanakin karshen mako ya fara tuntubar jama&#8217;a domin fitowa takarar kujerar gwamnan Kaduna.</p>
<p>Sunaye da masu mukaman da suka yi murabus yayin da suke son fitowa takara:</p>
<p>Kwara</p>
<p>A kalla kwamishinoni da hadiman Gwamna Abdulrahman Abdulrazaq na jihar Kwara ne suka yi murabus domin neman kujerun siyasa a zaben 2023.</p>
<p>Sun hada da:</p>
<p>1. Kwamishinan ilimi da cigaban dan Adam, Hajia Sa&#8217;adatu Modibbo-Kawu</p>
<p>2. Kwamishinan sha&#8217;anin hada-hada, Hajia Fatimah Arinola Lawal</p>
<p>3. Mai bai wa gwamna shawara na musamman kan ayyuka na musamman, Alhaji Yinka Aluko</p>
<p>. Mataimaki na musamman ga gwamnatin kan habaka ma&#8217;adanai, Dr Mohammed Abubakar</p>
<p>5. Kwamishinan shari&#8217;a, Salman Jawondo</p>
<p>6. Kwamishinan hakar ma&#8217;adanai, Harriet Afolabi-Osatimehin</p>
<p>7. Mai bada shawara na musamman kan tallafin al&#8217;umma, Kayode Oyin-Zubair</p>
<p>8. Babban manajan KWASSIP, Mohammed Brimah</p>
<p>9. Kwamishinan lafiya, Dr Raji Razak</p>
<p>10. Alhaji Abdulateef Alakawa, mai bada shawara ga gwamna kan lamurran siyasa</p>
<p>11. Kwamishinan ayyukan noma, Sabba Yisa Gideon</p>
<p>Kano</p>
<p>A kalla kwamishinoni 10 ne suka yi murabus, sun hada da:</p>
<p>1. Kwamishinan ruwa, Sadiq Wali</p>
<p>2. Mataimakin gwamna, Nasir Gawuna</p>
<p>3. Kwamishinan kananan hukumomi da lamurran sarautar, Murtala Suke Gari</p>
<p>4. Kwamishinan kasafi da tsaro, Alhaji Nura Muhammed Dankade</p>
<p>5. Kwamishinan yawon bude ido, Sanusi Said Kiru</p>
<p>6. Kwamishinan ayyuka na musamman, Ibrahim Ahmad Karate</p>
<p>7. Kwamishinan habaka karkara, Iliyasu Kwankwaso</p>
<p>8. Kwamishinan sufuri, Mahmoud Muhammad Santsi</p>
<p>9. Kwamishinan lafiya, Aminu Tsanyawa</p>
<p>10. Shugaban ma&#8217;aikatan fadar gwamna, Ali Haruna Makoda</p>
<p>Delta</p>
<p>A jihar nan, shugaban ma&#8217;aikatan fadar gwamnan da wasu kwamishinoni tara ne suka yi murabus.</p>
<p>Akwa Ibom</p>
<p>1. Kwamishinan habaka tattalin arziki, Akan Okon</p>
<p>2. Kwamishinan ayyukan gona, Glory Edet</p>
<p>3. Kwamishinan cinikayya da hannayen jarj, Baristw Prince Akpabio</p>
<p>4. Kwamishinan ayyuka na mhsamman, Okpulupm Etteh</p>
<p>5. Kwamishinan ayyuka, Farfesa Enoh Ibanga</p>
<p>6. Kwamishinan filaye da ruwa, Umo Eno</p>
<p>Benue</p>
<p>1. Shugaban ma&#8217;aikatan fadar gwamnatin, Fasto Terwase Orbunde</p>
<p>2. Sakataren yada labarai, Terver Akase</p>
<p>3. Kwamishinan yada labarai, al&#8217;ada da yawon bude ido, Ngunan Addingi</p>
<p>4. Kwamishinan muhalli da ruwa, Engr Dindo Ahire</p>
<p>5. Kwamishinan ilimi, Farfesa Dennis Ityavyar</p>
<p>6. Kwamishinan matasa da al&#8217;adu, Kwamared Ojemba Ojotu.</p>
<p>Rivers</p>
<p>1. Sakataren gwamnatin jihar, Dr Tammy Danagogo</p>
<p>2. Kwamishinan kudi, Isaac Kamalu</p>
<p>3. Kwamishinan wasanni, Boma Iyayi</p>
<p>4. Mai bai wa gwamnatin shawara na musamman kan ayyuka na musamman, George Kelly</p>
<p>5. Babban akawun jihar, Asimilaye Fubara.</p>
<p>Kaduna</p>
<p>Kwamishinan tsari da kasafi ne kadai, Mohammed Sani Abdullahi, wanda aka fi sani da Dattijo, shi ne mutum daya da yayi murabus.</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/sunayen-kwamishinoni-suka/" data-wpel-link="internal">Sunayen Kwamishinoni 53 da Suka yi Murabus Daga Mukamansu a Jahohi 7</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></content:encoded>
					
					<wfw:commentRss>https://hausa.arewaagenda.com/sunayen-kwamishinoni-suka/feed/</wfw:commentRss>
			<slash:comments>0</slash:comments>
		
		
		<post-id xmlns="com-wordpress:feed-additions:1">10193</post-id>	</item>
		<item>
		<title>Shugaba Buhari ya Aminci da Bude Sabbin Polytechnic a Jahohi 3</title>
		<link>https://hausa.arewaagenda.com/buhari-amince-bude-polytechnic/?utm_source=rss&#038;utm_medium=rss&#038;utm_campaign=buhari-amince-bude-polytechnic</link>
					<comments>https://hausa.arewaagenda.com/buhari-amince-bude-polytechnic/#respond</comments>
		
		<dc:creator><![CDATA[Khadija Garba]]></dc:creator>
		<pubDate>Tue, 12 Apr 2022 14:58:00 +0000</pubDate>
				<category><![CDATA[SIYASA]]></category>
		<category><![CDATA[Abia]]></category>
		<category><![CDATA[Delta]]></category>
		<category><![CDATA[Kano]]></category>
		<category><![CDATA[Polytechnic]]></category>
		<category><![CDATA[Shugaba Buhari]]></category>
		<guid isPermaLink="false">https://hausa.arewaagenda.com/?p=10144</guid>

					<description><![CDATA[<p>Shugaba Buhari ya Aminci da Bude Sabbin Polytechnic a Jahohi 3 Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da bude wasu sabbin Polytechnic guda uku a cikin wasu jihohi don saukaka wa mutane samun karatun gaba da sakandare. Darektan watsa labarai da hulda da jama’an Ma’aikatar Ilimi, Mr Ben Bem Goong ya bayyana hakan ta wata [&#8230;]</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/buhari-amince-bude-polytechnic/" data-wpel-link="internal">Shugaba Buhari ya Aminci da Bude Sabbin Polytechnic a Jahohi 3</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></description>
										<content:encoded><![CDATA[<p><strong>Shugaba Buhari ya Aminci da Bude Sabbin Polytechnic a Jahohi 3</strong></p>
<p>Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da bude wasu sabbin Polytechnic guda uku a cikin wasu jihohi don saukaka wa mutane samun karatun gaba da sakandare.</p>
<p>Darektan watsa labarai da hulda da jama’an Ma’aikatar Ilimi, Mr Ben Bem Goong ya bayyana hakan ta wata takarda da ya saki a Abuja.</p>
<p>A takardar ta ranar Talata ya ce Polytechnic din guda uku sun hada da na Umunnoechi a Jihar Abia, Orogun a Jihar Delta da kuma Kabo a Jihar Kano.</p>
<p>Abuja-Shugaban kasa Muhammadu Buhari ya amince da bude Kwalejojin Fasaha (Polytechnic) guda uku na tarayya a bangarori daban-daban na kasar nan a matsayin hanyar saukaka wa jama’a damar samun ilimin gaba da sakandare.</p>
<p>A wata takarda wacce Darektan watsa labarai da hulda da jama’a na Ma’aikatar Ilimi ta tarayya, Mr Ben Bem Goong ya saki a ranar Talata a Abuja ya shaida hakan.</p>
<p>A cewarsa Polytechnic din guda uku sun hada da na Umunnoechi da ke Jihar Abia, Orogun da ke Jihar Delta da Kabo a Jihar Kano, Nigerian Tribune ta ruwaito.</p>
<p>Mashawarcin shugaban kasa a bangaren kafafen watsa labarai na zamani, Bashir Ahmad shima ya tabbatar da rahoton kafa kwalejojin uku a shafinsa na Twitter.</p>
<p>Za su fara aiki a watan Oktoba mai zuwa</p>
<p>Nigerian Tribune ta nuna inda ya ce sabbin kwalejin na Fasaha din za su fara aiki ne a watan Oktoban 2022.</p>
<p>Idan aka tattara, yanzu haka akwai Foliteknik guda 36 na tarayya da ke cikin Najeriya.</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/buhari-amince-bude-polytechnic/" data-wpel-link="internal">Shugaba Buhari ya Aminci da Bude Sabbin Polytechnic a Jahohi 3</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></content:encoded>
					
					<wfw:commentRss>https://hausa.arewaagenda.com/buhari-amince-bude-polytechnic/feed/</wfw:commentRss>
			<slash:comments>0</slash:comments>
		
		
		<post-id xmlns="com-wordpress:feed-additions:1">10144</post-id>	</item>
		<item>
		<title>Sojojin Najeriya Sun Lalata Haramtattun Wuraren Tace Man Fetur 30 a Jahohi 3</title>
		<link>https://hausa.arewaagenda.com/sojoji-lalata-haramtattun/?utm_source=rss&#038;utm_medium=rss&#038;utm_campaign=sojoji-lalata-haramtattun</link>
					<comments>https://hausa.arewaagenda.com/sojoji-lalata-haramtattun/#respond</comments>
		
		<dc:creator><![CDATA[Khadija Garba]]></dc:creator>
		<pubDate>Fri, 08 Apr 2022 12:10:31 +0000</pubDate>
				<category><![CDATA[Taska]]></category>
		<category><![CDATA[bayelsa]]></category>
		<category><![CDATA[Delta]]></category>
		<category><![CDATA[man fetur]]></category>
		<category><![CDATA[Rivers]]></category>
		<category><![CDATA[Sojoji Najeriya]]></category>
		<guid isPermaLink="false">https://hausa.arewaagenda.com/?p=10134</guid>

					<description><![CDATA[<p>Sojojin Najeriya Sun Lalata Haramtattun Wuraren Tace Man Fetur 30 a Jahohi  3 Dakarun sojan Najeriya sun lalata haramtattun wuraren tace man fetur 30, sannan suka kwashe sama da lita miliyan 12 na gas na ɗin ababen hawa a ayyukan da suka yi a jihohin Delta, da Rivers da Bayelsa. Daraktan yada labarai na rundunar [&#8230;]</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/sojoji-lalata-haramtattun/" data-wpel-link="internal">Sojojin Najeriya Sun Lalata Haramtattun Wuraren Tace Man Fetur 30 a Jahohi 3</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></description>
										<content:encoded><![CDATA[<p><strong>Sojojin Najeriya Sun Lalata Haramtattun Wuraren Tace Man Fetur 30 a Jahohi  3</strong></p>
<p>Dakarun sojan Najeriya sun lalata haramtattun wuraren tace man fetur 30, sannan suka kwashe sama da lita miliyan 12 na gas na ɗin ababen hawa a ayyukan da suka yi a jihohin Delta, da Rivers da Bayelsa.</p>
<p>Daraktan yada labarai na rundunar sojan, Manjo Janar Bernard Onyeuko, shi ne ya bayyana haka a lokacin da yake zantawa da manema labarai ranar Alhamis a Abuja.</p>
<p>&#8220;Kamar yadda sanarwar tace, sojojin sun gano tare da lalata haramtattun wuraren tace mai 30, da tankunan ajiye 37, da tanda 31, da manyan jiragen ruwa na katako 12, da na&#8217;urorin sanyaya wuri biyu, da ramukan ajiya uku, da ganguna na ƙarfe,&#8221; a cewarsa.</p>
<p>“A dunkule, sojojin sun kwato litar mai miliyan 12, da tataccen litar gas 150,000, da lita 4,000 na danyen mai da aka sata, da motocin tanka uku, da motoci uku, da bututu 73, da babura biyu, da motar bas daya, da Toyota kirar Camry daya, da ƙirar Mercedes Benz daya.</p>
<p>“Bugu da kari, an kama wasu barayin manyan wayoyin wutar lantarki biyu da ke da alaka da lalatawa da kuma sata.&#8221;</p>
<p>&nbsp;</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/sojoji-lalata-haramtattun/" data-wpel-link="internal">Sojojin Najeriya Sun Lalata Haramtattun Wuraren Tace Man Fetur 30 a Jahohi 3</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></content:encoded>
					
					<wfw:commentRss>https://hausa.arewaagenda.com/sojoji-lalata-haramtattun/feed/</wfw:commentRss>
			<slash:comments>0</slash:comments>
		
		
		<post-id xmlns="com-wordpress:feed-additions:1">10134</post-id>	</item>
		<item>
		<title>&#8216;Yan Sanda 4 Sun Rasa Rayukansu Yayin da Tawagar Motar Ministocin Buhari ta yi Hatsari a Jahar Delta</title>
		<link>https://hausa.arewaagenda.com/yansanda-hatsari-tawagar/?utm_source=rss&#038;utm_medium=rss&#038;utm_campaign=yansanda-hatsari-tawagar</link>
					<comments>https://hausa.arewaagenda.com/yansanda-hatsari-tawagar/#respond</comments>
		
		<dc:creator><![CDATA[Khadija Garba]]></dc:creator>
		<pubDate>Wed, 09 Mar 2022 20:28:14 +0000</pubDate>
				<category><![CDATA[Labarai]]></category>
		<category><![CDATA[Babatunde Fashola]]></category>
		<category><![CDATA[Chris Ngige]]></category>
		<category><![CDATA[Delta]]></category>
		<category><![CDATA[Hatsari]]></category>
		<category><![CDATA[Ibrahim Gambari]]></category>
		<category><![CDATA[Shugaba Buhari]]></category>
		<category><![CDATA[yan sanda]]></category>
		<guid isPermaLink="false">https://hausa.arewaagenda.com/?p=9900</guid>

					<description><![CDATA[<p>&#8216;Yan Sanda 4 Sun Rasa Rayukansu Yayin da Tawagar Motar Ministocin Buhari ta yi Hatsari a Jahar Delta Daya daga cikin motocin da ke cikin ayarin shugaban ma’aikatan Buhari, Ibrahim Gambari, da minista Fashola da takwaransa Ngige sun yi hatsari a Asaba, jihar Delta. ‘Yan sanda hudu ne ake fargabar sun mutu a hatsarin wanda [&#8230;]</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/yansanda-hatsari-tawagar/" data-wpel-link="internal">&#8216;Yan Sanda 4 Sun Rasa Rayukansu Yayin da Tawagar Motar Ministocin Buhari ta yi Hatsari a Jahar Delta</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></description>
										<content:encoded><![CDATA[<p><strong>&#8216;Yan Sanda 4 Sun Rasa Rayukansu Yayin da Tawagar Motar Ministocin Buhari ta yi Hatsari a Jahar Delta</strong></p>
<p>Daya daga cikin motocin da ke cikin ayarin shugaban ma’aikatan Buhari, Ibrahim Gambari, da minista Fashola da takwaransa Ngige sun yi hatsari a Asaba, jihar Delta.</p>
<p>‘Yan sanda hudu ne ake fargabar sun mutu a hatsarin wanda aka ce ya faru ne da yammacin ranar Talata, 8 ga watan Maris.</p>
<p>Rahotanni sun ce manyan jami’an gwamnatin sun je babban birnin jihar Delta ne domin duba wata gada da aka gina.</p>
<p>Asaba, jihar Delta &#8211; Ayarin shugaban ma&#8217;aikata, Ibrahim Gambari; Ministan Ayyuka da Gidaje, Babatunde Fashola; da takwaransa na ma&#8217;aikatar kwadago da samar da aikin yi, Christ Ngige, sun yi hatsari a yammacin ranar Talata, 8 ga watan Maris.</p>
<p>Jaridar Punch ta ruwaito cewa hatsarin ya afku ne a yayin duba wata gada a garin Asaba na jihar Delta, inda rahoton ya kara da cewa ‘yan sanda hudu ne ake fargabar sun mutu.</p>
<p>An tattaro cewa direban motar ne ya rude yayin tuka motar da ke dauke da jami’an tsaro inda ta fada cikin wani rami mai zurfi.</p>
<p>Shaidun gani da ido sun bayyana yadda lamarin ya faru</p>
<p>Wani shaidan gani da ido, John Okorie, ya ce lamarin ya faru ne a lokacin da motar da ke dauke da wadanda lamarin ya rutsa dasu ke tattaunawa kan kwanar da ta kai ga wajen aikin gina gadar Neja ta biyu a Asaba.</p>
<p>An tattaro cewa motar ‘yan sandan ta yi gudu ne don haduwa da sauran tawagar motocin ministocin ne a lokacin da ta kauce daga titi kuma ta yi hatsari.</p>
<p>Har ila yau, wani direba a Delta, wanda bai bayyana sunansa ba, ya ce:</p>
<p>“Lamarin ya yi muni matuka.</p>
<p>“Direba dan sandan yana gudu yayin da ake tattaunawa kan lankwasar hanyar wanda saboda gudun ya kasa sarrafa motar. Suka fada cikin wani rami mai zurfi. Ni ina bin bayan ayarin, ina tuki na a hankali.</p>
<p>“Da taimakon wasu mutane mun ceto hudu daga cikinsu amma sun samu munanan raunuka. Suna ta ihu yayin da motar ta fado musu.”</p>
<p>Sai dai kakakin rundunar ‘yan sandan jihar Delta, DSP Bright Edafe, ya ce har yanzu bai samu rahoton faruwar hatsarin ba.</p>
<p>Karin bayani nan tafe&#8230;</p>
<p>&nbsp;</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/yansanda-hatsari-tawagar/" data-wpel-link="internal">&#8216;Yan Sanda 4 Sun Rasa Rayukansu Yayin da Tawagar Motar Ministocin Buhari ta yi Hatsari a Jahar Delta</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></content:encoded>
					
					<wfw:commentRss>https://hausa.arewaagenda.com/yansanda-hatsari-tawagar/feed/</wfw:commentRss>
			<slash:comments>0</slash:comments>
		
		
		<post-id xmlns="com-wordpress:feed-additions:1">9900</post-id>	</item>
		<item>
		<title>Jahohin Najeriya 12 da Gwamnatin Burtaniya ta Gargadi &#8216;Yan Kasar da su Guji Zuwa</title>
		<link>https://hausa.arewaagenda.com/burtaniya-gargadi-yankasar/?utm_source=rss&#038;utm_medium=rss&#038;utm_campaign=burtaniya-gargadi-yankasar</link>
					<comments>https://hausa.arewaagenda.com/burtaniya-gargadi-yankasar/#respond</comments>
		
		<dc:creator><![CDATA[Khadija Garba]]></dc:creator>
		<pubDate>Mon, 18 Oct 2021 19:01:21 +0000</pubDate>
				<category><![CDATA[Labarai]]></category>
		<category><![CDATA[adamawa]]></category>
		<category><![CDATA[Akwa Ibom]]></category>
		<category><![CDATA[bayelsa]]></category>
		<category><![CDATA[boko haram]]></category>
		<category><![CDATA[borno]]></category>
		<category><![CDATA[Burtaniya]]></category>
		<category><![CDATA[cross-river]]></category>
		<category><![CDATA[Delta]]></category>
		<category><![CDATA[Garkuwa]]></category>
		<category><![CDATA[gombe]]></category>
		<category><![CDATA[kaduna]]></category>
		<category><![CDATA[katsina]]></category>
		<category><![CDATA[Matsalar Tsaro]]></category>
		<category><![CDATA[najeriya]]></category>
		<category><![CDATA[Rivers]]></category>
		<category><![CDATA[Yobe]]></category>
		<category><![CDATA[zamfara]]></category>
		<guid isPermaLink="false">https://hausa.arewaagenda.com/?p=9336</guid>

					<description><![CDATA[<p>Jahohin Najeriya 12 da Gwamnatin Burtaniya ta Gargadi &#8216;Yan Kasar da su Guji Zuwa &#160; Gwamnatin Burtaniya ta gargadi &#8216;yan kasar da su guji zuwa jahohi 12 a Najeriya, inda ta ce akwai yiwuwar kungiyar Boko Haram ta yi garkuwa da &#8216;yan kasashen waje. Ofishin jakadancin Burtaniya da ke Abuja ya ce akwai bayanan da [&#8230;]</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/burtaniya-gargadi-yankasar/" data-wpel-link="internal">Jahohin Najeriya 12 da Gwamnatin Burtaniya ta Gargadi &#8216;Yan Kasar da su Guji Zuwa</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></description>
										<content:encoded><![CDATA[<p><strong>Jahohin Najeriya 12 da Gwamnatin Burtaniya ta Gargadi &#8216;Yan Kasar da su Guji Zuwa</strong></p>
<p>&nbsp;</p>
<p>Gwamnatin Burtaniya ta gargadi &#8216;yan kasar da su guji zuwa jahohi 12 a Najeriya, inda ta ce akwai yiwuwar kungiyar Boko Haram ta yi garkuwa da &#8216;yan kasashen waje.</p>
<p>Ofishin jakadancin Burtaniya da ke Abuja ya ce akwai bayanan da ya samu cewa ana shirin kaddamar da satar &#8216;yan kasashen waje da sunan neman kuɗin fansa ko kuma siyasa.</p>
<p>Jahohin sun haɗa da Borno da Yobe da Adamawa da Gombe da Kaduna da Katsina da Zamfara da Delta da Bayelsa da Rivers da Akwa Ibom da kuma Cross River.</p>
<p>Ofishin ya kuma kara da cewa an hari ma&#8217;aikatan jin-kai a wasu hare-hare da aka kaddamar arewa maso gabashin Najeriya, da suka haɗa da na garin Manguno a ranar 13 ga watan Yunin 2020.</p>
<p>Wani ɓangaren sanarwar ya kuma ce &#8220;yanayin tsaro ya kara tabarbarewa a arewa maso gabashin Najeriya tun 2018, kuma akwai yiwuwar sace ma&#8217;aikata &#8216;yan kasashen waje&#8221;.</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/burtaniya-gargadi-yankasar/" data-wpel-link="internal">Jahohin Najeriya 12 da Gwamnatin Burtaniya ta Gargadi &#8216;Yan Kasar da su Guji Zuwa</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></content:encoded>
					
					<wfw:commentRss>https://hausa.arewaagenda.com/burtaniya-gargadi-yankasar/feed/</wfw:commentRss>
			<slash:comments>0</slash:comments>
		
		
		<post-id xmlns="com-wordpress:feed-additions:1">9336</post-id>	</item>
		<item>
		<title>Corona: Cutar ta Kashe ƙarin Mutane 35 a Najeriya</title>
		<link>https://hausa.arewaagenda.com/corana-kara-kashe-mutane/?utm_source=rss&#038;utm_medium=rss&#038;utm_campaign=corana-kara-kashe-mutane</link>
					<comments>https://hausa.arewaagenda.com/corana-kara-kashe-mutane/#respond</comments>
		
		<dc:creator><![CDATA[Khadija Garba]]></dc:creator>
		<pubDate>Sun, 17 Oct 2021 11:14:45 +0000</pubDate>
				<category><![CDATA[Taska]]></category>
		<category><![CDATA[bauchi]]></category>
		<category><![CDATA[Corona]]></category>
		<category><![CDATA[Delta]]></category>
		<category><![CDATA[ekiti]]></category>
		<category><![CDATA[kaduna]]></category>
		<category><![CDATA[Kano]]></category>
		<category><![CDATA[kwara]]></category>
		<category><![CDATA[legas]]></category>
		<category><![CDATA[nasarawa]]></category>
		<category><![CDATA[NCDC]]></category>
		<category><![CDATA[ondo]]></category>
		<category><![CDATA[oyo]]></category>
		<category><![CDATA[Plateau]]></category>
		<category><![CDATA[Rivers]]></category>
		<category><![CDATA[Sokoto]]></category>
		<guid isPermaLink="false">https://hausa.arewaagenda.com/?p=9307</guid>

					<description><![CDATA[<p>Corona: Cutar ta Kashe ƙarin Mutane 35 a Najeriya &#160; Hukumar NCDC mai yaƙi da cutuka masu yaɗuwa a Najeriya ta ce cutar korona ta kashe ƙarin mutum 35 cikin kwana ɗaya. Cikin rahoton da ta wallafa, hukumar ta ce wasu ƙarin mutum 376 sun harbu da cutar. Mutanen da suka kamun sun fito ne [&#8230;]</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/corana-kara-kashe-mutane/" data-wpel-link="internal">Corona: Cutar ta Kashe ƙarin Mutane 35 a Najeriya</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></description>
										<content:encoded><![CDATA[<p><strong>Corona: Cutar ta Kashe ƙarin Mutane 35 a Najeriya</strong></p>
<p>&nbsp;</p>
<p>Hukumar NCDC mai yaƙi da cutuka masu yaɗuwa a Najeriya ta ce cutar korona ta kashe ƙarin mutum 35 cikin kwana ɗaya.</p>
<p>Cikin rahoton da ta wallafa, hukumar ta ce wasu ƙarin mutum 376 sun harbu da cutar.</p>
<p>Mutanen da suka kamun sun fito ne daga jaha 14 na ƙasar. Su ne:</p>
<p>Legas (215)</p>
<p>Rivers (82)</p>
<p>Ondo (16)</p>
<p>Imo (14)</p>
<p>Plateau (12)</p>
<p>Kaduna (10)</p>
<p>Kwara (9)</p>
<p>Ekiti (4)</p>
<p>Bauchi (3)</p>
<p>Delta (3)</p>
<p>Kano (3)</p>
<p>Sokoto (3)</p>
<p>Nasarawa (1)</p>
<p>Oyo (1)</p>
<p>Ya zuwa yanzu, jumillar mutum 209,173 ne aka tabbatar sun harbu da cutar a Najeriya. Kazalika ta kashe 2,804, sai kuma 197,084 da aka sallame su bayan sun warke.</p>
<p>The post <a href="https://hausa.arewaagenda.com/corana-kara-kashe-mutane/" data-wpel-link="internal">Corona: Cutar ta Kashe ƙarin Mutane 35 a Najeriya</a> appeared first on <a href="https://hausa.arewaagenda.com" data-wpel-link="internal">Arewa Agenda Hausa</a>.</p>
]]></content:encoded>
					
					<wfw:commentRss>https://hausa.arewaagenda.com/corana-kara-kashe-mutane/feed/</wfw:commentRss>
			<slash:comments>0</slash:comments>
		
		
		<post-id xmlns="com-wordpress:feed-additions:1">9307</post-id>	</item>
	</channel>
</rss>

<!--
Performance optimized by W3 Total Cache. Learn more: https://www.boldgrid.com/w3-total-cache/?utm_source=w3tc&utm_medium=footer_comment&utm_campaign=free_plugin

Page Caching using Disk: Enhanced 

Served from: hausa.arewaagenda.com @ 2026-04-06 13:54:25 by W3 Total Cache
-->