APC ta Sauke Shugabannin Jam’iyyarta
An tsawaita wa’adin kwamitin rikon kwaryan uwar jam’iyyar APC karkashin Buni.
An sallami tsohon mataimakin Oshiomole, Hilliard Eta, wanda ya shigar da jam’iyyar kotu.
Za’a shirya taron gangamin jam’iyyar nan da watanni shida.
Read Also:
Majalisar zartaswa, NEC, na jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta sauke dukkan shugabannin jam’iyya na dukkan matakai a fadin tarayya.
Wannan ya hada da shugabannin jam’iyyar na jihohi, yankuna da kasa.
Thisday ta ruwaito cewa gwamnan jihar Kaduna, Malam Nasir El-Rufa’i ya bayyana hakan yayin hira da manema labarai a fadar shugaban kasa bayan ganawar majalisar ranar Talata.
El-Rufa’i ya sanar da hakan ne tare da takwarorinsa na Imo da Ondo, gwamna Hope Uzodinma, da gwamna Rotimi Akeredolu.