Ba za mu Bari a yi Katsalanda ba a Zabukan 2023 – Shugaba Buhari

 

Shugaba Muhammadu Buhari ya yi alwashin cewa ba zai bari wani mahaluki ya kawo katsalanda ba a zabukan 2023 da ke tafe a Najeriya.

Buhari ya ce shugabancin da ba a ginata kan turbar gaskiya ba ba za ta kawo kasar alfanu ba.

Shugaban ya bayyana hakan ne lokacin da yake tarbar gwamnonin jam’iyyar APC da gwamnan Jihar Kebbi, Atiku Bagudu ke jagoranta a fadarsa da ke Abuja.

Shugaban Najeriyar ya kuma ce a karkashin shugabancinsa, zai ci gaba da mutunta ‘yan Najeriya ta hanyar tabbatar da cewa kuri’unsu sun yi tasiri saboda suna da yancin zabar shugabannin da suke so a dukkan matakai.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here