Shugaba Buhari ya Karɓi Baƙuncin Tinubu a Fadarsa da ke Abuja 

 

Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya karɓi baƙuncin jagoran jam’iyyarsu ta APC, Bola Ahmed Tinubu, a fadarsa da ke Abuja ranar Lahadi.

Da isarsa ne kuma suka wata ganawa cikin sirri.

Tsohon gwamnan na Legas ya ce ya kai wa Buhari ziyara ne domin ya gode masa.

“Na zo ne na gode wa Shugaba Buhari saboda ziyarar da ya kai mani a Landan lokacin da nake jinyar ƙafa. Ya nuna mani ƙauna. Shugaba ne na musamman,” in ji shi.

A watan Agusta ne Buhari ya ziyarci Tinubu bayan an yi masa tiyata a ƙafarsa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here