2022: Shugaba Buhari zai Gabatar da Kasafin Kudin ga Majalisa
Shugaban Najeriya Muhammadu Buhari ya shiryawa gabatarwa majalisa da kasafin kudin 2022 a ranar Alhamis.
Read Also:
Mataimakin shugaban majalisar dattijai, Ovie Omo-Agege, ne ya shaida hakan a wannan Talatar a zauren majalisar.
Ya bukaci kwamitin harkokin kudi na majalisar ya gaggauta aikin da yake yi kan tsare-tsaren kasafi da kudade, domin gabatar da rahotonsu gaban majalisa zuwa gobe Laraba.