Ya Kamata Gwamnati ta Samar da Runduna ta Musamman Don Kare Makarantu – Atiku Abubakar
Biyo bayan sace daliban wata makarantar sakandare a Zamfara, Atiku Abubakar ya yi martani.
Ya bayyana cewa, ya kamata gwamnati ta samar da runduna ta musamman don kare makarantu.
Ya kuma bayyana kokensa kan yawaitar sace dalibai a yankunan Arewa maso yammacin Najeriya.
Tsohon mataimakin shugaban kasa, Atiku Abubakar, ya ba da shawarar kirkiro da sabuwar rundunar ‘yan sanda don kare makarantu daga hare-haren ‘yan bindiga a yankunan da lamarin tsaro yake kara ta’azzara.
Read Also:
Ya fadi hakan ne yayin da yake mayar da martani kan sace dalibai 73 da aka yi kwanan nan a Makarantar Sakandaren Gwamnati ta Kaya dake Karamar Hukumar Maradun a Jahar Zamfara.
Tsohon dan takarar shugaban kasaN na jam’iyyar PDP ya kuma koka kan harin da sace daliban.
A wani rubutu da ya yi a shafinsa na Facebook, Atiku ya bayyana cewa:
“Ina bakin ciki da rahotannin sake sace dalibai a Zamfara. Ga yankin da ke tasowa a fagen ilimi mai mahimmanci, ci gaba da kai hari kan ci gaban mu ba abin yarda bane.
“Watakila lokaci ya yi da za a kirkiri Sashin Jira da Kare Makarantu na musamman don kare makarantu a yankunan da ke fuskantar wadannan hare-hare.
“Idan ba mu dauki matakan riga-kafi ba, ina tsoron cewa ilimi a yankunan da suke dama a lalace na iya fuskantar asarar da ba za a iya gyara ta ba.
“A halin yanzu, ina fatan ana duk wani kokari da za a yi don ganin an dawo da daliban cikin hanzari.”