Hukumar INEC ta Rufe Yin Rijistar Zaɓe

 

Ƴan Najeriya da dama suna ƙorafi kan rashin samun damar yin rijistar zaɓe, bayan da hukumar zaɓe mai zaman kanta ta rufe yin rijistar a jiya Lahadi.

INEC ta ce ba za ta sake buɗe ci gaba da yin rijistar ba, bayan da ta tsawaita hakan a baya.

Sai dai rahotanni sun ce ko a jiya Lahadin wuraren da ake yin rijistar sun yi cikar kwari, amma har ma’aikatan INEC suka tashi mutane da dama ba su samu yi ba.

Tun a watan Yunin shekarar 2021 ne INEC ta fara yi wa ƴan Najeriya rijistar, sai dai duk da hakan ba a kai ga kammalawa ba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here