Kungiyar ISWAP ta Kashe Mayakan Boko Haram 87 a Borno

 

Kungiyar ISWAP ta kai hari kan mayakan Boko Haram a wani lamari mai kama da ɗaukar fansa a yankin Tafkin Chadi.

Hakan na zuwa ne kwana biyar bayan da wasu mayaƙan Boko Haram suka kashe mayaƙan ISWAP 24 a Tsaunukan Mandara da Gaba a garin Gwoza na jahar Bornon Najeriya, kamar yadda kafar yaɗa labaran PRNigeria ta rawaito.

Mayaƙan ISWAP ɗin sun kai harin ne sansanin kwamandan Boko Haram Bakoura Modou a yankin Tafkin Chadin a jiya.

PRNigeria ta ce mayaƙan ISWAP ɗin sun far wa sansanin Boko Haram ɗin ne a cikin wasu kwale-kwlae masu tsananin gudu har 50.

“An kashe fiye da mayaƙan ISWAP 87 a faɗan, a cewar kafar PRNigeria.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here