Dukan ‘Yarsa : ‘Yan Sanda Sun Kama Mahaifin da ya yi Hayar ‘Yan Daba Don su Doki Malamin
Rundunar ‘yan sanda sun cafke wani mutum bisa laifin kai ‘yan daba makarantar ‘yarsa don su doki malami.
 Rahotanni sun bayyana cewa, malamin ya daki ‘yar mutumin ne, lamarin da ya bata masa rai sosai.
 A halin yanzu mutumin da shi da ‘yan daban suna hannun ‘yan sanda ana ci gaba da bincike.
Abeokuta, Ogun – Rundunar ‘yan sandan jahar Ogun ta kama wani mutum mai shekaru 35, Abidemi Oluwaseun da laifin hayar ‘yan daba don kai hari kan wani malami saboda ya lakadawa ‘yarsa mai shekaru 15 duka.
 Rahotanni sun bayyana cewa Oluwaseun ya dira kwalejin ‘yan mata ta Baptist dake Idi-Aba a Abeokuta tare da ‘yan daba biyu a ranar Talata 12 ga watan Oktoba don tunkarar wani malamin da ya zarga da dukan ‘yarsa.
Jami’in hulda da jama’a na rundunar ‘yan sandan jahar, DSP Abimbola Oyeyemi ne ya bayyana hakan a ranar Talata a cikin wata sanarwa, Punch ta rawaito.
Oyeyemi ya ce an cafke wanda ake zargin tare da wasu mutum biyu; Fayesele Olabanji mai shekaru 25, da Alebiosu Quawiyu mai shekaru 24.
Jami’in ya kara da cewa ‘yan sanda sun samu kiran gaggawa ne daga shugaban makarantar.
Oyeyemi ya ce ‘yan sanda sun yi nuni da cewa wasu mutane uku sun dira makarantar da motar da ba ta da rajista, dauke da sabbin adduna kuma suna barazanar yi wa malamin makarantar lalata.
Ya ce:
“Bayan kiran gaggawa, DPO, reshen Kemta, CSP Opebiyi Sunday, ya tattara mutanensa ya tafi wurin da aka kama mutanen uku a harabar makarantar.
 An kwato mota Toyota da ba a yi wa rajista ba da kuma adda.
Yadda lamarin ya faru
Sanarwar da take bayyana yadda lamarin ya faru, Oyeyemi ya bayyana cewa:
 “Malamin bayan ya gano wadanda ke tayar da hankali a aji ya yi musu bulala a matsayin ladabtarwa, amma ‘yar wanda ake zargin ta tafi gida ta kai karar abin da ya biyo baya inda mahaifinta ya hada ‘yan daba guda biyu suka kutsa makarantar da adda.”
Oyeyemi duk da haka ya ce Kwamishinan ‘yan sanda, Lanre Bankole, ya ba da umarnin a binciki wadanda ake zargi da kyau kuma a gurfanar da su da kotu da cikin gaggawa.
 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here