Jahar Kano ta fi ko Ina Zaman Lafiya a Najeriya – Gwamna Ganduje

Ganduje ya bayyana wasu irin matakan da gwamnatinsa ta dauka kan tsaro a Kano.

Ministan tsarin Najeriya, Salihi Magashi, ya ce Najeriya na cikin halin kakanikaye.

A cewar Ganduje, jahar Kano ta fi ko ina zaman lafiya a Najeriya Gwamnan jahar Kano, Abdullahi Ganduje, a ranar Litinin ya bayyana cewa jahar Kano ta fi kowace jiha tsaro a Najeriya bisa matakan da gwamnatinsa ke dauka.

Ya yi alhinin matsalar rashin tsaro a Najeriya, musamman na karshen makon da ya gabata inda aka kaiwa gwamnan Benue, Samuel Ortom, hari. The Nation ta rahoton Ganduje ya yi wannan jawabi bayan ganawarsa da shugaba Muhammadu Buhari a fadar shugaban kasa dake Abuja.

Yace: “Abinda na sani shine a yau jahar Kano ce jaha mafi lumana a fadin tarayya kuma ba haka kawai bane, lallai akwai matakan tsaron da muke dauka, misali hadin kai tsakanin jami’an tsaro a Kano.”

“Mun samar da cibiyar leken asiri; CCTV inda muke kallon abinda ke faruwa cikin birnin Kano, mune masu na’urar bibiyan motoci mafi karfi a Kano.”

“A dajin Falgore inda yan bindiga ke zama, muka sam, ba zamu yarda a Kano ba. Mun kafa sansanin horon Soji a dajin saboda kada yan bindiga su zauna.”

Ganduje ya kara da cewa a Iyakar Kano da Kaduna, akwai daji a wajen kuma sun kafa wani shirin Ruga, sun tattauna da Fulanin daji, kuma sun amince zasu zauna wajen.

“Mun dauki dukkan wadannan matakai ne don samar da zaman lafiya a Kano,” Ganduje ya kara.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here