Kungiyar Tagwaye ta Jahar Kano ta Gudanar da Babban Taro a Jahar

 

Ƙungiyar Tagwaye ta Jahar Kano ta gudanar da babban taronta na shekara-shekara kuma kyawawan hotunan membobinta sun haska kafofin sada zumunta.

A cewar shugaban kungiyar, an kafa gidauniyar domin ta saukaka matsalar tagwaye da ke jahar ‘Yan Najeriya a kafafen sada zumunta sun mayar da martani kan wannan ci gaban Kungiyar tagwaye ta jahar Kano ta sa mutane tofa albarkacin bakunansu a shafukan sada zumunta bayan gudanar da babban taronta na shekara -shekara.

Da yake magana da BBC Pidgin, shugaban kungiyar da aka bayyana a matsayin Hassan Tijjani Salihu ya ce sun tattauna yadda za a taimaki juna a cikin al’umma.

A cewar Salihu, kungiyar ta kafa wata gidauniya don taimakawa tagwaye da ke da matsala a jahar. An yada kyawawan hotunan tagwaye a jahar a kafafen sada zumunta kuma ‘yan Najeriya sun mayar da martani kan hotunan.

Yawancin tagwayen sun yi kama da junansu kuma kowannensu ya sa tufafi iri ɗaya.

Da yake magana game da ƙungiyar, marubucin Najeriya Richard Ali ya rubuta a Facebook:

“Tabbas dole ne ƙungiyar tagwaye ta kasance tana da kwamiti na dindindin kan sasanta rigingimu? Domin mu ‘yan daddaya ba za mu kuskura mu tsoma baki ba a lokacin da Hassana da Hussaina ke musayar zazzafan kalamai ba.”

Ga wasu daa cikin martanin jama’a a shafin Instagram:

@maamie_pehbles ta ce:

” 2 2 Allah ya halicci kowa da kowa.”

@ominiaho yayi sharhi:

“Menene manufa da hangen wannan ƙungiyar?”

@tams__k ya ce:

“Zan ji wani iri idan zan ga sama da tagwaye 50 a cikin daki. Zan tsorata… idona zai juya.”

@passwordng yayi sharhi:

“Ba da daɗewa ba za su gabatar da buƙatu ga gwamnati.”

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here