Majalisar Dattawa ta Amince da Naɗa Mutane 20 a Matsayin Masu Bayar da Shawara ga Tinubu

 

Majalisar dattawan Najeriya ta amince da naɗa mutum 20 da shugaban ƙasar Bola Ahmed Tinubu ya aike mata domin amincewarta ya naɗa su a matsayin mashawartansa.

Matakin na zuwa ne bayan da shugaban ya aike wa majalisar wasiƙar neman amincewa majalisar domin naɗa mutanen.

To sai dai a wasiƙar da shugaban majalisar dattawan ƙasar Sanata Ahmad Lawan ya karanto a gaban majalisar a lokacin zamanta na ranar Talata, babu sunayen mutanen a cikinta.

Amma ana kallon sabbin naɗe-naɗen da shugaban ƙasar zai yi a matsayin wata manuniya kan inda alƙiblar gwamnatinsa za ta fuskanta wajen magance tarin matsalolin da ƙasar ke fuskanta kama daga matsalar tsaro da tattalin arziki.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com