Dole Musulmi da Kirista su Haɗa ƙarfi da ƙarfe Wajen Goya wa Falasɗinawa Baya – Fani-Kayode

Tsohon Ministan Sufurin Jiragen Saman Najeriya, Cif Femi Fani-Kayode ya ce dole Musulmi da Kirista baki ɗaya su haɗa ƙarfi da ƙarfe wajen goya wa Falasɗinawa baya.

Ya bayyana hakan ne a taron Ranar Aƙsa da ƙungiyar wayar da kan Musulmi ta Muslim Awareness International (MAI) wanda ya gudana a Filin Wasa na ƙasa da ke Surulere a Legas.

Sauran waɗanda suka yi jawabi a wajen taron sun haɗa da darakta a MURIC Farfesa Lakin Akintola da Sheikh Sheikh Dhikrullahi Shafi’i.

Fani-Kayode ya daɗe yana caccakar Isra’ila a kan kisan kiyashin da ya ce tana yi wa Falasɗinawa, sannan ya ƙara da cewa Musulmi da Kiristan Najeriya dole su goya wa Falasɗinawa baya a ƙoƙarin Isra’ila na mamaye zirin Gaza.

A cewarsa, “an kasha maza da mata da ƙananan yara. An kashe Musulmi da Kirista, an tarwatsa Masallatai da Coci-coci. Suna yunƙurin shafe komai ne,” kamar yadda muka kalato daga jaridar Daily Trust.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Logged in as Khadija Garba. Log out?

Please enter your comment!