Mutanan da Sukai Dace a Mulkin Buhari
Akwai wasu ‘Yan Najeriya da su ka samu manyan mukamai na Duniya
Da dama daga cikinsu tsofaffin Ministoci ne da aka yi a gwamnatin kasar – Wanda ake sa ran za ta zama sabuwar shiga a jerin it ace Okonjo-Iweala A cikin ‘yan shekarun bayan nan, an samu wasu mutanen Najeriya da ubangiji ya tsaga da rabonsu, su ka rike muhimman mukumai da ake ji da su a Duniya.
Wannan ruwan kujeru da aka yi wa ‘yan Najeriya ya zo ne a mulkin shugaba Muhammadu Buhari, wanda kasashen Duniya ke yi masa kallon dattijon kwarai.
1. Amina J. Mohammed
Read Also:
Amina Mohammed mai shekaru kusan 60 ce mataimakiyar shugabar majalisar dinkin Duniya. Tsohuwar ministar ta hau wannan kujera ne a farkon 2017 bayan nada António Guterres. Miss Mohammed ta ajiye kujerar Minista a Najeriya bayan ta samu wannan babbar kujera.
2. Tijjani Bande
A shekarar 2019 ne majalisar dinkin Duniya ta zabi wani mutumin Najeriya a matsayin shugaban zauren majalisa. Tijjani Bande ya sauka daga kan wannan kujera bayan shekara guda a 2020. Farfesan ya fito ne daga jihar Kebbi, kafin nan shi ne wakilin Najeriya a majalisar dinkin Duniya.
3. Akinwumi Adesina
Wani mutumin Najeriya da ke cikin wannan jeri shi ne Dr. Akinwumi Adesina wanda ya taba rike kujerar ministan gona da raya karkaka a lokacin da D. Goodluck Jonathan ya ke mulkin kasar. Akinwumi Adesina ya zama shugaban bankin cigaban Afrika har kuma ya samu ya zarce.
4. Ngozi Okonjo-Iweala
A halin yanzu kusan duka kasashen kungiyar Turai da Afrika su na goyon bayan Okonjo-Iweala.