Ambaliyar Ruwa: Mutane 80 Sun Rasa Rayukansu a Sudan

 

Fiye da mutane 80 sun rasa rayukansu, tun bayan fara damuna a watan Yuli a Sudan.

Mai magana da yawun hukumar kare fararen hula ta kasar ya ce fiye da mutane 67 sun samu raunuka.

Ambaliyar dai ta shafi larduna 14 cikin 18 na kasar, yayin da ta rusa gidaje dubu 30.

Gonaki da dama da gine-ginen gwamnati sun lalace.

Majalisar Dinkin Duniya ta ce ambaliyar ta shafi aƙalla mutane dubu dari da biyu a dukkan sassan ƙasar.

A bara ne hukumomi a Sudan suka ayyana dokar ta ɓaci ta tsawon wata uku saboda ambaliyar da ta hallaka mutane 100 a shekarar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here