Mutane 7 Sun Rasu Sakamakon Rushewar Gini a Abuja

 

Aƙalla mutum bakwai ne suka rasu sakamakon ruhsewar wani gini a babban birnin tarayyar Najeriya, Abuja.

Muƙaddashin darakta-janar na hukumar bada agajin gaggawa ta Abuja FEMA, Abdulrahman Mohammed ne ya bayyana hakan a lokacin da ya kai ziyara wajen ginin da ya rushe a kan titin hanyar tafiya filin jirgin sama.

Ya ce lamarin ya auku ne a ranar Asabar a sanadiyar wasu da suka shiga ginin, wanda hukumar kula da ingancin gine-gine ta Abuja take rusawa domin cire ƙarafa, kamar yadda Channels ta ruwaito.

Ya ce bayan waɗanda suka rasu, akwai wasu mutum da suke jinya a asibiti, sannan ya gargaɗi mutane su guji jefa rayukansu cikin hatsari ta hanyar shiga cikin gine-ginen da aka rusa.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Logged in as Khadija Garba. Log out?

Please enter your comment!