Dakarun Soji Sun Sake Gano ‘Yar Chibok Tare da ‘Danta a Borno

Dakarun soji na rundunar Hadin kai, da ke yaki da Boko Haram a Najeriya, sun tabbatar da sake gano wata ‘yar makarantar Chibok mai suna Ruth Bitrus, wacce ta kubuta daga hannun mayakan Boko Haram tare da danta.

Jaridar Daily Trust a Najeriya ta ruwaito babban kwamandan dakarun rundunar, Manjor janar GC Musa na bayyana hakan ranar Laraba.

A lokacin da yake mika wasu magunguna da hukumar raya yankin arewa maso gabas ta bai wa sojojin da ke aiki a yankin.

Kwamandan ya ce ”Idan za ku iya tunawa makonni da suka gabata, mun kubutar da ‘yan matan Chibok biyu, to yanzu ma mun sake kubutar da wata guda daya”

A ‘yan kwanakin baya ne dai, dakarun suka kubutar da ‘yan mata biyu a karamar hukumar Gazuwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here