Ƙungiyar SERAP ta Caccaki Gwamnatin Tarayya Kan Rufe Harkokin Karatu na Tsawon Lokaci

 

A yau Litinin 4 ga watan Yuli, ɗalibai suka shiga kwana na 140 a gida tun bayan fara yajin aikin ƙungiyar malaman jami’o’i ASUU.

Ƙungiyar SERAP da wasu ƙungiyoyin ilimi a Najeriya, sun caccaki gwamnatin tarayya karkashin shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari.

Ƙungiyoyin sun nuna sakacin FG da ƙin cika alƙawari ne suka jawo rufe harkokin ilimi a manyan makarantu.

Abuja – Ƙungiyar Socio-Economic Rights Accountability Project (SERAP) da wasu ƙungiyoyin fafutuka kan ilimi a Najeriya, sun caccaki gwamnatin shugaban ƙasa, Muhammadu Buhari, kan rufe harkokin karatun makarantun gaba da Sakandire na tsawon lokaci.

Punch ta rahoto cewa yajin aikin da kungiyar malaman jami’o’i (ASUU) ta tsunduma ya shiga kwana na 140 yau Litinin, yayin da yajin aikin manyan ma’ikata da kanana na jami’o’i ya shiga kwana na 68.

Yayin da yanzu haka shugabannnin ƙungiyar kwalejin fasa ke gudanar da taro a Jigawa bayan janye yajin aikin gargaɗi na mako biyu, ƙungiyar malaman kwalejin ilimi sun tsunduma yajin aikin watanni biyu.

A wata sanarwa da ta fito ranar Lahadi, mataimakin daraktan SERAP, Kolawole Oluwadare, yace gazawar FG na cika bukatun ASUU, ƙin aiwatar da yarjejeniyar da ta cimma da kungiyar ya bar ‘ya’yan talakawa a gida yayin da yan siyasa suka tura yaran su makarantun kuɗi.

Oluwadare ya ce:

“Rashin daidaito a ɓangaren ilimi ya haifar da sakamako mai illa, kuma ga dukkan alamu a haka za’a cigaba har gaba. Bayan kasancewarsa dama a karan kansa, samun damar yin ilimi makulli ne ga wasu damarmakin.”

“Ilimi ke samar da murya wacce ake fafutukar kare haƙƙi da dama, idan babu ilimi mutane ba zasu iya cimma wasu abubuwa masu amfani ba da suka shafi rayuwa.”

“Idan mutane suka samu ilimi, za su yi amfani da kwarewa da kwarin guiwa wajen kwato haƙƙoƙin su. Ilimi na baiwa mutane karfin samun bayanai kan nauyin da ya rataya kan gwamnati.”

Wasu ƙungiyoyin ilimi biyu sun bi sahun SERAP baya

Da yake jawabi a wata hira da wakilin mu ranar Lahadi, shugaban ƙungiyar fafutukar gyara ilimi a Najeriya, Ayodamola Oluwatoyin, ya soki shirun manyan masu ruwa da tsaki game da rufe harkokin karatu.

Oluwatoyin ya ce:

“Abun takaici ne gwamnati ta kama hannunta ta bari ana tattaunawar da babu alamar sasantawa. Wajibi fadar shugaban ƙasa cikin gaggawa ta karɓi ragamar tattauna wa da ƙungiyoyin nan.”

Haka nan kuma, shugaban ƙungiyar Education Rights Campaign, Michael Lenin, ya ce: “Wajibi a ɗora laifin wannan yajin aikin kungiyoyin wanda ya dakatar da harkokin ilimi a wuyan gwamnati.”

“Abu ne da bamu saba gani ba cewa dukkan manyan ƙungiyoyin makarantun gaba da Sakandire suna yajin aiki; hakan ya nuna yadda gwamnatoci masu biye wa juna suka ɓarnata ɓangaren ilimi ta fannin kuɗi.”

Wane hali ake ciki game da yajin aikin?

Duk wani yunkuri na jin ta bakin ministan kwadugo da samar da ayyukan yi, Dakta Chris Ngige, bai yi nasara ba. Ngige a ayyana ƙanshi a matsayin ministan sasanci tsakanin FG da ƙungiyoyin.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here