Mun Kashe ‘Yan IPOB 2 Mun Kama 5 – Rundunar Sojin Najeriya

Hadin gwiwar dakarun Bataliya ta rundunar sojin Najeriya, ‘yan sandan Najeriya da kuma jami’an tsaro na farin kaya sun kashe mayakan IPOB/ESN guda biyu tare da kama wasu biyar bayan wata mumunar arangama da suka yi a ranar Litinin 17 ga watan Yuli 2023 a unguwar Fuji Junction,Asaba, Delta state.

Ganawar ta biyo bayan kiraye-kirayen al’ummar garin suka yi da kai ƙaran ‘yan ta’adda sun kai wa garin hari, inda dakarun hadin gwiwa suka mayar da martani cikin gaggawa.

‘Yan ta’addan sun kasa jurewa hadin gwiwar dakarun da karfin wutar da sukayi ta sakewa inda wasu mutane biyu daga cikin su suka mutu cikin harbe-harben sojojin, yayin da wasu kuma suka tsere zuwa maboyarsu da ke kusa da kogin Okpanam.

Amma dakarun da ke fafatawa da ‘yan ta’addan sun yi nasarar bibiyar su a wani gida da ke kusa da kogin Okpanam, inda suka kama su.

Sojojin sun kuma kwato makamai da dama daga ƴan ta’addan.

Muna rokon jama’a da su ci gaba da ba jami’an tsaro hadin kai ta hanyar samar da bayanan da suka dace don tallafa wa ayyukansu na tunkarar kalubalen tsaro.

Babban hafsan sojin kasa, Manjo Janar Taoreed Lagbaja, ya yaba wa rundunar da hadin gwiwar da suka yi, ya kuma bukace su da su ci gaba da yin hakan, domin dawo da zaman lafiya da kwanciyar hankali a yankin.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here