Bisa Kuskure: Sojojin Najeriya Sun Kashe Yara 7 Tare da Jikkata 5

 

Sojojin Najeriya sun yi kuskuren kashe yara bakwai tare da jikkata wasu biyar a wani harin sama da suka kai a yankin Maradi na Jamhuriyyar Nijar, kamar yadda gwamman yankin ya shaida wa kamfanin dillacin labaran Faransa.

Gwamnan Maradi Chaibou Aboubacar, ya ce hare-haren sama da sojojin Najeriya suka kai ya rutsa da yara a ƙauyen Nachade a ranar Juma’a.

Gwamnan ya ce suna tunanin sojojin Najeriya sun yi kuskuren kisan yaran ne a ƙoƙarin kai wa ‘yan bindiga a yankunan kan iyaka hari.

Babu dai wata sanarwa daga rundunar sojin Najeriya game da al’amarin.

Gwamnan Maradi ya ce lamarin ya shafi yara ne guda 12, kuma bakwai daga cikin sun mutu yayin da biyar ska jikkata.

A cewar gwamnan, harin ya rutsa da yaran ne suna cikin wasa yayin da iyayensu ke hidimar biki.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here