Tawagar Kano Pillars ta yi Hatsari, Mutane 3 Sun Samu Raunuka

 

Tawagar ‘yanwasan ƙwallon ƙafa ta Kano Pillars ta yi hatsari a kan hanyarsu ta zuwa birnin Jos na jihar Filato.

Ƙungiyar ta ‘yan ƙasa da shekara 19 ta tafi Jos ne domin buga wasan mako na biyar da Plateau U-19 a gasar matasa.

“‘Yanwasa da yawa da kuma direban motar sun ji raunuka a hatsarin kuma nan take aka kai su asibiti,” a cewar wani saƙo da ƙiungiyar ta wallafa a shafinta na X.

Ta ƙara da cewa “cikin sa’a babu wanda ya rasu kuma tawagar likitoci na ci gaba da saka ido”.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here