Allah ya yi wa Tsohon Kocin Super Falcons, Ismaila Mabo ya Rasuwa

Tsohon kocin tawagar ƙwallon ƙafar mata ta Najeriya ‘Super Falcons’ Ismaila Mabo ya rasu yana da shekara 79 a duniya.

Kafofin yaɗa labaran ƙasar sun ruwaito cewa tsohon kocin ya rasu ne bayan wata jinya mai tsanani a gidansa da ke birnin Jos da ke jihar Plateau ta tsakiyar ƙasar.

Marigayin ya jagoranci tawagar Super Falcons zuwa gasar Kofin Duniya ta mata a shekarar 1999 da gasar wasannin Olympics a shekarar 2000 da 2004.

A shekarar 1999 ya jagoranci tawagar wajen samun nasarar da ba ta taɓa samu ba a tarihin wasan Kofin Duniya inda ta kai wasan zagayen kusa da ƙarshe.

A shekarar 1998 ya taimaka wa tawagar matan lashe kofin ƙasashen Afirka ta mata ‘AWCON’, bayan da suka zura ƙwallaye 28 a gasar.

Haka kuma a shekarar 2000 ya jagoranci tawagar wajen kare kofin ƙasashen Afirka ‘AWCON’ da aka yi a Afirka Kudu.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here