Shugaban Ukraine ya Sake Kira ga Gwamnatocin ƙasashen Yammaci da su ba Shi Makamai

 

Shugaban Ukraine Volodymyr Zelensky ya yi kira ga gwamnatocin ƙasashen yammaci su ba shi jirage da tankokin yaƙi da makaman kakkabo makami mai linzami.

A jawabin da shugaban ya yi mai sosa rai, ya ce manyan makaman da ya kamata a kare ƴancin Turai da su na can a jibge sun yi ƙura.

Mr Zelensky ya yi koken cewa ba a iya kakkabo jiragen Rasha da bindiga.

“Me Nato take yi? Shin Rasha ce ke jagorantarta? Me suke jira? Kwana 31 yanzu. Abin da kawai muke nema kashi ɗaya na abin da Nato ta mallaka,” in ji shugaban.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here