‘Yan kwallon Najeriya da Zasu kara da Sierra Leone

Yayinda ake saura kwanaki uku wasan kwallon fidda gwanin gasar kofin nahiyar Afrika wanda akafi sani da AFCON.

tsakanin Najeriya da Sierra Leone, gwarazan yan wasan Super Eagles sun dira jihar Edo.

Yan kwallon a yau sun motsa jiki a filin kwallon San Ogbemudia dake birnin Benin tare da mataimakin gwamnan jihar Edo, Philip Shaibu.

Daga cikin yan wasan da suka hallara a cewar NFF sune:

Ahmed Musa

William Troost-Ekong

Alex Iwobi

Ola Aina

Joe Aribo

Leon Balogun

Kevin Akpoguma

Sebastin Osigwe

Zaidu Sanusi

Tyronne Ebuehi

Etebo Oghenekaro

Maduka Okoye

Ikechukwu Ezenwa

Chidozie Awaziem

Kelechi Iheanacho

Emmanuel Dennis

Wanna itace wasa ta farko da yan kwallon Najeriya zasu buga domin samun gurbin shiga sahun kasashen da zasu kara a gasar Afcon 2022.

Za’a buga wasanni biyu tsakanin dukkan kasashe; daya a gida, daya a waje.

A wasar farko, Najeriya zata karbi bakuncin yan kwallon kasar Sierra Leone a filin kwallon Samuel Ogbemudia dake birnin Benin, jihar Edo.

Za’a buga wasar ranar Juma’a, 13 ga watan Nuwamba, 2020.

Bayan haka yan kwallon Najeriya zasu garzaya filin kwallon Siaka Stevens dake Freetown, kasar Sierra Leone ranar 17 ga Nuwamba, 2020.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here