Cutar Amai da Gudawa Tayi Sanadiyyar Kashe Mutane 6 a Jahar Kano

 

Gwamnatin jahar Kano ta tabbatar ta ce wata bakuwar cuta da ta bulla a jahar ta yi sanadin rasuwar mutane shida.

Kwamishinan lafiya na jahar, Dr Aminu Ibrahim-Tsanyawa ne ya tabbatar da hakan a ranar 7 ga watan Mayu.

Ibrahim-Tsanyawa ya ce ma’aikatar lafiya tana bincike a kan cutar da nufin gano matsalar yayin da ake jinyar sauran wadanda suka kamu.

Gwamnatin jahar Kano a ranar Litinin ta tabbatar da cewa mutane shida sun mutu sakamakon wata bakuwar cuta a karamar hukumar Minjibir a jahar, Vangaurd ta ruwaito.

Kwamishinan lafiya na jahar Kano, Dr Aminu Ibrahim-Tsanyawa wanda ya tabbatar da hakan ya ce wasu mutum 46 da suka kamu da cutar na jinya a asibiti.

Ibrahim-Tsanyawa ya ce cutar ta bulla ne a kauyen Gandun Koya da ranar 7 ga watan Mayu kuma ta yadu zuwa garuruwan da ke makwabtaka da ita.

“Ana danganta bullar cutar da yin bayan gida a fili da rashin tsaftace muhalli a garuruwan. “Wadanda cutar ta kamu da su suna amai da gudawa.

“Cutar ta kashe mutane shida, an sallami 28 daga asibiti yayin da sauran 18 suna nan suna jinya a asibitin,” in ji shi.

Ibrahim-Tsanyawa ya ce ma’aikatar lafiya na jihar ta fara bincike domin gano abin da ya yi sanadin wannan cutar mai daure kai.

A yayin da ya ke jadada kokarin gwamnatin jahar wurin cigaba da wayar da kan mutane da kiyayewa, Ibrahim-Tsanyawa ya bukaci mutanen garin su rika tsaftace muhallinsu da jikinsu don takaita yaduwar cutar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here