Ambaliyar Ruwa ta Lalata Hekta Sama da 115,000 a Najeriya

 

Najeriya na ci gaba da fama da matsalar karancin abinci, yayin da sabbin bayanai daga cibiyar bayar da agajin gaggawa ta kasa (NEOC) suka nuna cewa ambaliyar ruwa ta lalata gonaki sama da hekta 115,000 a faɗin ƙasar.

Jihohi 29 da ƙananan hukumomi 154 ne abin ya shafa, inda sama da mutum 611,000 lamarin ya shafa kai tsaye, mutum 225,169 suka rasa matsugunansu, gidaje 83,457 ne suka lalace, mutum 201 ne kuma suka rasa rayukansu sannan mutum 2,119 kuma suka samu raunuka a bana.

Wannan bayanin na ambaliya ya zo ne a daidai lokacin da ake fama da ƙarancin abinci da kuma ƙaruwar hauhawar farashin kayan abincin, wanda hukumar kididdiga ta Najeriyan (NBS) ta bayyana ya hau sama da kashi 40 cikin 100.

Wani sabon bincike da babban bankin Najeriya CBN ya gudanar daga ranar 22 zuwa 26 ga Yulin 2024 ya nuna cewa, hauhawar farashin kayayyaki zai tilastawa magidanta a Najeriya kashe mafi yawan kuɗaɗen shigarsu kan abinci nan da watanni shida masu zuwa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here