Ambaliyar Ruwa ta Tafi da Gidaje 200 a Jihar Kebbi

 

Hukumomi a jihar Kebbi da ke arewa maso yammacin Najeirya sun ce gwamman mutane ne suka rasa matsugunansu sakamakon rushewar kusan gidaje 200, bayan wata mumunar ambaliyar ruwa da aka fuskanta a yankin karamr hukumar Arugungu.

Shugaban karamar hukumar Argungu Hon. Aliyu Sani Gulma ya shaida wa BBC cewa mamakon Ruwan sama da aka fuskanta a karshen mako ne ya haifar da ambaliyar.

Ya kuma ce ambaliyar ta shafi ƙauyuka huɗu a yanikin na karamar hukumar ta Arugungu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here