Ambaliyar Ruwa: Za a yi Mamakon Ruwan Sama na Kwana Biyar a Jihohi 21 – NIMET

 

Gwamnatin Tarayyar Najeriya ta yi hasashen cewa mamakon ruwan sama da za a yi kwana biyar ana yi, zai janyo ambaliyar ruwa a wurare 123 na jihohi 21 na ƙasar.

Rahoton ya bayyana jihohin Benue da Kogi da Anambra da Delta da Rivers da Imo da Bayelsa a matsayin jihohin da iftila’in zai fi ƙamari.

Jaridar Punch a Najeriya ta ruwaito cewa wani rahoto da hukumar kare muhalli ta fitar ya yi kira ga mazauna waɗanann jihohi riƙa sanya idanu tare da lura da al’amura.

Gwamnatin ta kuma bayyana cewa yankuna 123 ne za su iya fuskantar ambaliyar, wadda ake hasashen zai faru tsakanin 4 ga Satumba zuwa 8 ga Satumba.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here