Ambaliyar Ruwa: Kadoji da Dama sun Kuɓuce a China

 

Mahukuntan ƙasar China sun bayyana cewa, wasu kadoji sun tsere daga wani gandu da ake kiwata su a kudancin ƙasar, lokacin da guguwar Haikui ta haddasa ambaliya.

Kadoji kusan 75 ne suka kuɓuce lokacin da wani tafki mai suna Maoming a lardin Guangdong ya yi ambaliya.

Yayin da aka kame wasu, hukumomin yankin sun ce sun harbe wasu “saboda tsaro”.

Kafofin yaɗa labaran ƙasar sun ba da rahoton cewa, ya zuwa yanzu an tattara dabbobin guda takwas.

An gargaɗi mazauna ƙauyen da ke kusa da lardin, su zauna a gidajensu.

Guguwar Haikui ta shafe sama da mako ɗaya tana ɓarna a kudancin Asiya, inda ta shafi China da Hong Kong da Taiwan da kuma Japan.

Mutum 7 ne suka mutu yayin da wasu uku suka ɓace bayan guguwar kuma ta haddasa zabtarewar ƙasa da ambaliya a kudancin China.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com