Amurka na Jagorantar Atisayen Soji na Kwana 15 a Ghana da Ivory Coast

 

Amurka na jagorantar wani atisayen soji na kwana 15 a ƙasashen Ghana da Cote d’Ivoire.

Atisayen wanda aka fara ranar 1 ga watan Maris ya ƙunshi sojoji 1,300 daga ƙasashe 30 na duniya.

Atisayen wanda aka yi wa laƙabi da “Flintlock 2023” an shirya shi ne da nufin ƙarfafa wa ƙasashen duniya gwiwwa wajen yaƙar ƙungiyoyin ta’addancin tare da haɗin gwiwwa a kan iyakokin ƙasashe.

Tun shekarar 2005 ne Amurka ke jagorantar atisayen soji a yankin yammacin Afirka duk shekara.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here