Kundin Tsarin Mulkin Jam’iyyar APC ya Bada Zabi Uku na Yadda za’a Gudanar da Zaben Fidda Gwani

 

Jam’iyyar All Progressives Congress (APC) ta yi watsi da tsarin kato bayan kato wajen zaben fidda gwanin takarar shugaban kasa na zaben 2023 sabanin yadda tayi a zaben 2019.

Jam’iyyar ta yanke shawarar amfani da deleget wajen zaben wanda zai wakilci jam’iyyar a zaben shugaban kasa.

An yanke shawarar haka ne a taron Majalisar zartaswa NEC ta 11 da ya gudana a Transcorp Hotel a watan Afrilu a birnin tarayya Abuja.

Kundin tsarin mulkin jam’iyyar APC ya bada zabi uku na yadda za’a gudanar da zaben fidda gwani.

Ittifaki, yar tinke wanda aka fi sani da kato bayan kato, da kuma na deleget.

Jam’iyyar APC na da Deleget 7,800.

Yayinda jihar Kano tafi yawan deleget, Abuja ke da mafi karanci.

Legit ta tattaro muku adadin deleget da kowace jiha ke da shi:

Kano: 465

Katsina: 384

Borno:324

Osun: 308

Lagos: 304

Oyo: 292

Jigawa: 266

Niger: 251

Ogun: 248

Nasarawa: 245

Abia: 154

Adamawa: 184

Akwa Ibom: 165

Anambra: 163

Bauchi: 202

Bayelsa: 79

Benue: 180

Cross River: 194

Delta: 170

Ebonyi: 154

Edo: 168

Ekiti: 216

Enugu: 131

Gombe: 134

Imo: 236

Kaduna: 234

Kebbi 213

Kogi: 222

Kwara: 195

Ondo: 200

Plateau: 185

Rivers: 151

Sokoto: 193

Taraba: 146

Yobe: 222

Zamfara: 169

FCT: 53

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here