Karɓa-Karɓa: Atiku ya yi Kira da a yi wa Mulkin Najeriya Garambuwal

 

Tsohon mataimakin shugaban Najeriya Alhaji Atiku Abubakar ya yi kira da a yi wa kundin tsarin mulkin ƙasar garambawul domin mayar da mulkin ƙasar na karɓa-karɓa a tsakanin yankunan ƙasar guda shida.

Atiku, wanda shi ne ɗantakarar PDP a zaɓen shugaban ƙasa da aka yi bara ya kuma yi kira da a mayar da shugabancin ƙasar ya zama zango ɗaya na shekara shida maimakon zango biyu na shekara huɗu-huɗu.

Atiku ya aike da buƙatar hakan ne ga kwamitin gyara kundin tsarin mulkin ƙasar na Majalisar Dattawa, wanda ya fara zama domin yi wa kundin na 1999 garambawul ƙarƙashin jagorancin mataimakin shugaban majalisar dattawa sanata Barau I. Jibrin, kamar yadda muka kalato daga jaridar Daily Trust.

Haka kuma ya buƙaci a yi gyara a ɓangaren mafi ƙarancin matakin karatun masu neman shugabanci, da sauransu.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here