Buhari Bashi da Kwarewar da Zai Iya Magance Matsalolin Najeriya – Tanko Yakasai

 

Dattijon kasa Yakasai ya bayyana karara irin mummunan kuskuren da ‘yan Najeriya suka tafka.

Ya ce, babban kuskure ne da ‘yan Naajeriya suka zabi shugaba Buhari da zimmar magance matsaloli.

Ya kuma ce, Buhari bashi da kwarewar da zai iya magance matsalolin Najeriya, kuma ba ya goyon bayan Buhari.

Dattijo dan kasa Alhaji Tanko Yakasai, ya ce zaben Manjo Janar Muhammadu Buhari a matsayin shugaban kasar shi ne babban kuskure da ‘yan Najeriya suka tafka a ‘yan shekarun nan.

Yakasai, wanda ya yi magana ta musamman ga Sunday Tribune, ya ce ya san cewa Buhari ba shi da iko da kuma iyawar isar da magance matsalolin kasar.

“Ban taba goyon baya kuma ba zan goyi bayan Buhari ba. Na san Buhari ba shi da kwarewar da zai iya mulkin kasar nan. Ban taba canza ra’ayina game da rashin cancantarsa ta shugabancin kasar nan ba.

“Ban goyi bayan Buhari ba saboda na san ba zai iya magance matsalolinmu a matsayinmu na kasa ba. Ba wai kawai iya ake bukata ba. Zan shiga kokarin neman wanda zai magance mana matsalolinmu.

“Babu wanda zai iya magance matsalolin Najeriya har sai an samu wani shiri na magance matsalolin.

“Da yawa yanzu suna son zama shugaban kasa saboda suna son samun iko da neman kudi ne.

“Irin wadannan mutane ba za su iya magance matsalolinmu ko matsalolin kowace kasa ba.

Mutanen da suka sanya tunaninsu kan matsalolin ne kadai za su iya magance irin wadannan matsalolin.

“Idan har muna son bunkasa harkar noma, dole ne mu samar da wani shiri wanda zai magance matsalolin bangaren.

“Dole ne a samu wani shiri don magance matsalolin wutar lantarki, kayayyakin more rayuwa da kuma shirin da zai samar da ayyukan yi ga matasa.

“Idan akwai shirye-shirye ga sassa daban-daban, ta makomar kasar za ta canza zuwa mafi kyau.

“Amma wadannan mutane suna son iko ne kawai don neman tara kudi. Ba batun Kudu ko Arewa bane domin duk ‘yan kudu da ‘yan arewa sun mulki kasar nan. Matsalar rashin shiri da iya aiki ne ke damun kasar,” inji shi.

Amma ya ce adawar da yake yi wa Shugaba Buhari ba zata zama fassara zuwa ga amincewa ga wadanda ke kiran a wargaza kasar ba, yana mai cewa za a samu karin matsaloli ga bangarorin daban-daban idan suka balle.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here