Tsaro: ‘Yan Burkina Faso na Nuna Fushi Kan Gazawar Gwamnatin Soji

 

Daya daga cikin hari mafi muni da ya janyo mutuwar darururwan mutane a Burkina Faso, ya janyo fushi daga yan kasar da ke ganin gazawar gwamnatin soji, da ta lashi takobin kawo karshen matsalolin tsaron da kasar ke fama da su.

Masu dauke da makamai ne suka kashe mutanen sama da 400 a ranar 24 ga watan Agustan nan a wani kauye da ake kira Barsologho, da ke arewa maso tsakiyar kasar, lokacin da suke haka ramukan buya, da sojoji suka basu shawarar samarwa.

Wannan mummunan hari mai tayar da hankali, a iya cewa shine mafi muni, tun bayan da kungiyar da ke da alaka da alkaida ta yadu daga Mali zuwa Burkina Fason, a wajajen shekarar 2015.

Wannan mummunan kaye ne ga gwamnatin soja ta Ibrahim Traore, wadda ta ce za ta kawo karshen kungiyar ko ana há maza há mata. Bayan wannan hari, gwamnatin tabatarrar da lallai na rasa rayuka, to amma ta ki bayar da adadin wadanda suka mutun.

Babban limamin cocin Katolica mafi girma a kasar da ke birnin Wagadugu Jean Emmanuel Konvolbo, ya yi Allah wadarai da gwamnatin sojin, yana mai bayyana martaninta a matsayin borin kunya.

A cewarsa ‘’Rashin daukar mataki game da irin wadannan kashe kashe da ake samu dai dai yake da taimakawa masu yunkurin karar da bani adama, dole ne kowa ya nuna takaicinsa’’.

Wata kungiyar yan uwan wadanda harin ya rutsa da su dai ta ce adadin wadanda suka mutum ya haura mutum dari hudu.

Kunigyar ta zargi gwamnatin soja da kokarin rufe bakin duk wanda y aso nuna damuwa ko bacin rai game da abubuwan da ke faruwa a kasar, alhalin su kuma sun lullube komai.

Ta ba da misali da wani yunkuri da sojoji suka yi na kama wani dan gwagwarmaya da sautins aya yadu yana sukar sakacin da aka yi har aka kai harin.

Har ta kai ga jama’a suka shiga lamarin suka hana sojojin tafiya da shi ta karfi da yaji.

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here