CNG: ‘Yan Arewa Karmu Dogara da Gwamnati da Sojoji

Wasu kungiyoyin arewa sun bukaci al’umman yankin a kan su tashi tsaye don ba kansu kariya a yayinda lamarin tsaro ke kara tabarbarewa.

Kungiyoyin sun bayyana cewa daga yanzu al’umman yankin ba za su zauna suna jiran gwamnati da dakarun sojin kasar su karesu ba.

Hakan ya biyo bayan yankan rago da mayakan Boko Haram suka yi wa wasu manoma a garin Zabarmari da ke karamar hukumar Jere, jihar Borno.

Gamayyar kungiyoyin arewa a ranar Lahadi, 29 ga watan Nuwamba, sun jaddada kiransu ga al’umman garuruwan arewacin kasar a kan su tashi tsaye sannan su kare kansu.

Kungiyoyin sun yi kiran ne biyo bayan kisan kiyashin da aka yi wa manoma a garin Zabarmari, karamar hukumar Jere na jihar Borno.

Kakakin gamayyar, Abdul-Azeez Suleiman, ya ce yanzu ba za a iya dogara a kan gwamnati da dakarun sojin kasar don ba garuruwan arewa kariya ba, jaridar Daily Trust ta ruwaito.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here