An ɗage Sauraron Bayar da Belin El-Rufai

Babbar Kotun Tarayya da ke Jihar Kaduna ba ta yanke hukunci kan buƙatar beli da tsohon gwamnan jihar, Nasir El-Rufai, ya gabatar ba inda ta ce za ta sanar da matsayarta a ranar 14 ga watan Afrilu.

Wannan na zuwa ne bayan da kotun ta saurari hujjoji daga ɓangaren masu kare El-Rufai da kuma ɓangaren masu ƙara inda kowanne ɓangare ya gabatar da dalilansa kan ko ya dace a bayar da beli ko akasin haka.

Bayan kammala sauraron, alƘalin ya bayyana cewa akwai buƘatar ƙarin nazari kan bayanan da aka gabatar kafin yanke hukunci na karshe.

Abin da ya ja hankalin masu lura da al’amuran siyasa shi ne yadda ranar da aka sanya domin yanke hukuncin ta zo daidai da lokacin babban taron jam’iyyar ADC na kasa.

Haka kuma, kotun ta shirya cigaba da sauraron ƙara tsakanin El-Rufai da Gwamnatin Tarayya a ranar 23 ga Afrilu, 2026.

A makon da ya gabata ne hukumar ICPC ta gurfanar da El-Rufai a gaban mai shari’a Rilwan M. Aikawa kan tuhume-tuhume guda 10 da suka haɗa da zargin karkatar da kadarorin gwamnati da kuma halasta kuɗaɗen haram

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here