Ɗan sanda ya Rasa Ransa a Harin da ‘Yan Boko Haram Suka Kai wa Tawagar Shugaban Karamar Hukuma a Borno

Wasu yan bindiga da ake zargin yan Boko Haram ne sun kai wa jerin gwanon motoccin shugaban karamar hukumar Nganzai a Borno hari.

Mohammed Bashir Bukar, hadimin shugaban karamar hukumar Nganzai, Hon Asheikh Mamman ya ce mai gidansa lafiyarsa lau kuma ba a sace shi ba.

Bukar, amma ya ce jami’in dan sanda guda daya daga cikin tawagar ya riga mu gidan gaskiya sakamakon harin da yan ta’addan suka kai musu a hanyar su ta zuwa wani aiki.

Borno- Ɗan sanda ya riga mu gidan gaskiya a yayin da wasu da ake zargin yan Boko Haram ne suka kai wa tawagar motocin shugaban karamar hukumar Nganzai a Jihar Borno, Hon Asheikh Mamman Gadai, hari a ranar Laraba.

Lamarin ya faru ne a hanyar Gajiram da Gajiganna lokacin da Asheikh da tawagarsa ke hanyarsu ta zuwa wani aiki, rahoton Daily Trust.

Hadimin Asheikh ya tabbatar da afkuwar harin A cikin sanarwa, Mohammed Bashir Bukar, mataimaki na musamman ga shugaban karamar hukumar Nganzai a bangaren watsa labarai ya tabbatar da harin.

Sanarwar ta ce Hon Asheikh lafiyarsa kalau, ɗan sanda cikin tawagarsa ya rasu.

An bukaci al’umma su yi watsi da jita-jitar cewa yan ta’addan sun sace Hon Asheikh. Amma, sanarwar ba ta bada karin bayani game da harin ba.

An yi kokarin ji ta bakin Bukar a lokacin hada wannan rahoton amma ba a same shi ba.

A halin yanzu dai Najeriya na fama da matsalar rashin tsaro da ake yi wa kallon mafi muni a tarihin kasar.

Dakaci karin bayani…

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here