An Sake Gano Gawar Mutane 3 Cikin Wadanda Gini ya Ruftowa a Legas

 

Hukumar bayar da agajin gaggawar ta Najeriya ta ce an samu karin adadi na wadanda suka mutu sakamakon ruftawar wani gini a birnin Legas da ke kudu maso yammacin kasar.

Hukumar bayar da agajin gaggawa ta kasar ta shaida wa BBC cewa an samu karin gawarwaki uku a yau Litinin yayin da ake ci gaba da aikin ceto a wajen da ginin ya fadi.

A ranar Lahadi ne dai ginin mai hawa bakwai da ke tsakiyar birnin ya rufta

Kawo yanzu dai ba a bayyana dalilin ruftawar ginin ba.

A wata sanarwa da gwamnatin jihar ta fitar, ta ce kwamishinan tsara birane na jihar Dakta Idris Salaka ya yi murabus a wani matakin farko na sauya fasalin hukumar, an kuma gargadi duka sauran ma’aikatar hukumar da su girmama doka.

Faduwar gine-gine dai ba sabon abu ba ne a birnin Legas, inda ake zargin mazauna birnin da yin watsi da dokokin da hukumar tsare birane ta jihar ta gindaya kafin aiwatar da gini a birnin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here