Gwamnatin Ghana ta Rage Kuɗin Aikin Hajjin 2025

 

Gwamnatin Ghana ta sanar da rage kuɗin aikin Hajjin shekarar 2025 daga cedi 75,000 zuwa cedi 62,000, wanda yayi daidai da dala $4,130.

Wannan na daga cikin matakin cika alƙawarin da shugaban ƙasar, John Dramani Mahama ya yi a lokacin yaƙin neman zaɓe, inda ya sha alwashin rage kuɗin aikin hajji domin ƙara samar sauƙi ga musulmin Ghana wurin gudaanar da aikin hajji.

A makonnin da suka gabata ne dai shugaban ƙasar ya aika wata tawaga zuwa ƙasar Saudiyya, domin sabunta tattaunawa da mahukuntan ƙasar kan tsare-tsaren aikin hajjin bana ciki har da batun kuɗaɗe.

Matakin na zuwa ne a daidai lokacin da wasu ƙasashen ciki har da Najeriya suka yi ƙari a kan kuɗin aikin hajjin.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here