Gwamnan Jahar Abia ya yi Martani Kan Barin Jam’iyyar PDP

 

Gwamna Okozie Ikpeazu ya magantu a kan rade-radin cewa yana shirin sauya sheka.

Ikpeazu ya ce sam bai ga dalilin da zai sa ya bar PDP zuwa wata jam’iyya ba.

Ya kuma jadadda cewa sune da karfi a jihar Abia.

Gwamnan jihar Abia, Okozie Ikpeazu ya bayyana cewa ba zai sauya sheka daga jam’iyyar Peoples Democratic Party (PDP) zuwa All Progressives Congress (APC).

Da yake watsi da rade-radin sauya shekar, ya ce batun bai da tushe saboda PDP ce jam’iyya mafi rinjaye a jihar, jaridar The Nation ta ruwaito.

Da yake magana a Umuahia, babbar birnin jihar, Ikpeazu ya ce bai ga dalilin da zai sa ya bar PDP zuwa wata jam’iyya ba.

Ya ce: “Ban ga dalilin da zai sa na bar PDP zuwa wata jam’iyyar siyasa ba. Yadda ake murza kambun siyasa a kowani jiha ya banbanta da juna.

“A nan Abia, mutanen sun gamsu da PDP kuma ina ganin takarar Ndi Abia zai cimma nasara a karkashin inuwar jam’iyyar PDP.”

Ikpeazu ya kara da cewa: “Babu wanda ya iya gamsar dani cewa akwai wata jam’iyya a nan Abia da ta fi PDP. Ni babban dan PDP ne kuma jigo a jam’iyyar.

“Bugu da kari, ni ne mataimakin Shugaban kungiyar gwamnonin PDP. Na gwammaci na zama kwandastan mota da na zama direban motar da bata tafiya.”

 

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here