ICPC ta Gano Ayyukan Mazabu da Aka Karkatar a Fadin Najeriya da Kudinsu ya Kai N2.8bn

 

Hukumar da ke yaki da cin hanci da almundahanar kudade ta ICPC a Najeriya ta ce ta gano ayyukan mazabu da aka karkatar a fadin kasar da kudinsu ya kai Naira biliyan 2.8

Hukumar ta ce ta gano hakan ne ta hanyar wani kwamiti da ta kafa don bin diddigin ayyukan mazabu a fadin kasar.

Wanda ya gano ayyukan mazabu kusan 2,444 da aka karkatar da kudinsu tsakanin shekarar 2019 zuwa 2021.

Yayin da yake yake gabatar da takaitaccen kundin binciken hukumar a birnin Legas, daraktan gudanarwa na hukumar Akeem Lawal, ya ce a karon farko an gano ayyukan mazabu 524 a jihohi 12 da babban birnin tarayya a shekarar 2019.

Sannan kuma a karo na biyu, kwamitin bin diddigin ya gano ayyukan mazabu 822 a jihohi 16 a shekarar 2020,

Haka kuma a karo na uku na bin diddigin an zakulo ayyukan mazabu 1,098 a jihohi 17 hade da Abuja babban birnin kasar.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here