Bayan Cire Tallafi: Man fetur ya Tashi a Kasar Kenya

 

Farashin man fetur ya kai matsayin da bai taba kai wa ba a kasar Kenya bayan da kasar ta fara aiwatar da matakin cire masa tallafi.

A ranar Laraba hukumar kula da makashin kasar ta ce ta cire tallafi a kan man fetur, yayin da za ta ci gaba da bayar da karamin tallafi kan gas da kalanzir

A yanzu farashin litar man fetur a kasar ya kai Shilin 179, a maimakon shilin 160 da ake sayar da shi a baya.

Matakin na zuwa ne bayan da sabon shugaban kasar William Ruto a jawabin rantsuwar kama aikinsa, ya bayyana cewa gwamnatinsa za ta cire tallafin mai da na kayan abinci a kasar.

To sai dai akwai fargaba game da cewa cire tallafin kacokan zai haifar wa da tattalin arzikin kasar koma baya, yayin da farashin man fetur din zai shafi tsadar rayuwa kai tseye.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here