Hukumar zabe ta kasa reshen jihar Kano ta bayar da sanarwa a hukumance cewar Gwamnan jihar Kano, Abdullahi Umar Ganduje ne ya lashe zaven Gwamnan jihar Kano da aka gudanar a ranar 23 ga watan Maris din nan.

Ganduje ya fadi a zaven farko da aka yi a ranar9 ga watan Maris, inda Abba Kabiru Yusuf na jam’iyyar PDP ya kayar da shi da sama da kuri’u 26,000′ sai dai kuma Gwamnan ya lashe zaven zagaye na biyu da aka kuma yi a wasu mazabu da aka soke a zaben farko.

Gwamnan Ganduje ya samu kuri’u 45,876 a zagaye na biyu da aka yi na zaben Gwamnan Kano, inda Abba Kabiru Yusuf na jam’iyyar PDP samu 10,239.

The post INEC ta ce Ganduje ne ya lashe zaben Gwamnan Kano appeared first on Daily Nigerian Hausa.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here