Adadin Mutanen da Aka Kama Masu Fasa Shaguna da Sunan Zanga-Zanga a Kano da Jihar Nasarawa

 

An sa dokar hana zirga-zirga ta awa 24 a Kano bayan zanga-zangar tsadar rayuwa ta rikide zuwa tarzoma a jihar.

Hakan na zuwa ne bayan ’yan sanda sun kuma kama mutane 269 kan fasa shaguna da sace kayan ciki a lokacin zanga-zangar.

Daga cikin mutanen da aka kama har da matasan da suka dauki makami tare da tayar da rikici a yayin zanga-zangar a rana Alhamis.

Kakakin ’yan sanda a Jihar Kano, wanda ya gabatar da wadanda ake zargin ya bayyana cewa sun raunata jama’a tare da lalata dukiyoyin jama’a da kayan gwamnati a yayin zanga-zangar da ta rikide zuwa bore.

hannunsu da suka hada da kayan abinci da sauransu da suka kwashe a wuraren da suka fasa.

A cewarsa, wadanda ake zargin za su ci gaba da kasancewa a tsare zuwa lokacin da shashen binciken laifuka na rundunar zai kammala bincike domin garfanar da su a gaban shari’a.

An kama 25 a Jihar Nasarawa

A Jihar Nasarawa kuwa, mutane 25 ne aka kama bisa zargin fasa shaguna da kwashe kayan jama’a lokacin zanga-zangar tsadar rayuwa a garin Keffi.

Kwamishinan ’yan sandan jihar, Umar Shehu-Nadada, ya shaida wa wakilinmu cewa an shawo kan masu zanga-zangar..

A cewarsa, bata-gari da kananan yara na daga cikin wadanda suka shiga zanga-zangar suka haddasa rikici.

A jihar dai, an sanya dokar hana fita a yankin Mararaba da wasu garuruwa da ke Karamar Hukumar Karu sakamakon tashin rikici.

Shugaban Karamar Hukumar, James Thomas, ya sanar da haramta zirga-zirga daga karfe 6 na yamma zuwa 6 ba safe a wuraren.”

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here