Wanda Suka Kara Kawo Matsalar Rashin Tsaro – Sanata Ita Enang

Ita Enang ya zargi Gwamnonin Neja-Delta da azalzala wutar rikicin yankin.

Sanata Enang yace Gwamnonin Jihohi suka sa ake samun rikici a Neja-Delta.

Hadimin Shugaban kasar yace al’ummar ba su amfana da karin kason 13%.

Babban mai ba shugaban kasa Muhammadu Buhari shawara a kan harkokin Neja-Delta, Ita Enang, ya yi magana game da harkar rashin tsaro.

Sanata Ita Enang ya zargi gwamnonin jihohin yankin Neja-Delta da kasa a gwiwa wajen samar da tsaro.

A yau ne jaridar Daily Trust ta rahoto hadimin shugaban kasar yana zargin gwamnonin jihohi masu arzikin fetur da rashin kawo zaman lafiya.

Sanata Enang ya bayyana haka ne yayin da kungiyar DROAN ta masu matatar danyen mai a Najeriya suka kai masa wata ziyara a ofishinsa.

Enang ya ce: “Gwamnonin sun yi sanadiyyar da yankunan da ke da danyen mai ba za su zaunu ba,” Ya ce a dalilin haka ake da matsalar rashin tsaro.

Da yake jawabi a gaban ‘ya ‘yan kungiyar DROAN, Enang ya ce karin kason kudin da ake ba yankin sam bai yi amfani wajen kawo cigaba ba.

Ya ce: “Gwamnonin bangaren Neja-Delta sun kawo matsalar rashin tsaro saboda kin amfani da kason 13% wajen kawowa yankunansu cigaba.”

A dokar kasa, ana ware karin kudi na musamman wajen rabon kason FAAC, wanda ake ba duk wata jiha da ta ke da arzikin man fetur a Najeriya.

Mai ba shugaban kasa shawara, Ita Enang, ya taba rike kujerar Sanata a Akwa Ibom, jihar da ta fi kowace arzikin mai a kasa, kafin ya koma APC.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here