Hukumar Kare Hakki Bil Adama na Bincike Kan zargin kisa a Zaɓen Fidda Gwanin APC a Kano

 

Hukumar kare hakkin bil adama ta kasa da haɗin gwiwar kungiyoyin farar-hula a Kano sun kaddamar da kwamitin bincike kan zargin kisan mutane uku a zaɓen fidda gwanin da APC ta gudanar a Kano.

Jaridar Daily Trust ta Najeriya ta rawaito yadda wani mai takarar gwamna a inuwar jam’iyyar APC, Sha’aban Sharada, ya zargi cewa an kashe magoya bayansa da jikkata da dama a lokacin zaɓen fitar da gwani da aka gudanar ranar Alhamis.

Kwamitin mutane 11 da aka naɗa karkashin jagoranci, Shehu Abdullahi na hukumar kare hakkin bil’adama da Ibrahim Waiya na ƙungiyar farar-hula a Kano.

Waiya ya ce ana saran kwaimitin ya gabatar da rahoton da ya tattara nan da mako uku domin gaggauta bincike.

Sannan an samu wata gamayar kungiyoyin farar-hula a Kano da su ma suka bukaci a soke zaɓen fitar da gwani na APC kan zargin tafka kura-kurai da aringizo.

Mataimakin gwamnan Kano, Nasiru Yusuf Gawuna ne dai ya lashe zaɓen bayan doke abokin takararsa Sha’aban Ibrahim Sharada.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here