Bayan Dakatar da Shi: Zan Cigaba da Kasancewa Mai Kwazo da Tasiri a APC – Oshiomhole

 

An soke umurnin kotu wanda ya dakatar da Adams Oshiomhole a matsayin shugaban jam’iyyar APC.

Oshiomhole ya bayyana hakan ne a lokacin da yake zantawa da manema labarai a ranar Lahadi, 29 ga watan Agusta, game da matsayinsa a cikin jam’iyya mai mulki.

Tsohon gwamnan na Edo ya kara da cewa duk da cewa an cire shi daga mukaminsa, ba zai yi kasa a gwiwa ba wajen ci gaba da kasancewa memba na jam’iyyar APC.

Abuja – Tsohon shugaban jam’iyyar All Progressives Congress (APC) na kasa Adams Oshimhole, yayi magana game da zama memba na jam’iyya mai mulki da kuma wasu hujjoji game da dakatar dashi daga ofis.

Oshiomhole ya ce kotun daukaka kara ta soke dakatarwar da aka yi masa a matsayin shugaban APC, makwanni biyu bayan da aka ba da umarnin farko, PM News.

Kalamansa:

“An yanke hukuncin kotun ne a ranar 2 ga watan Yuli, 2020, kusan makonni biyu bayan an cire ni daga ofis. Na yanke shawarar bayyana shi ne saboda na ga masu sharhi da yawa suna ba da shawarar cewa mutane ba su san cewa an yi watsi da karar ba.”

Tsohon gwamnan na Edo wanda ya ce har yanzu shi dan APC ne mai himma ya lura cewa ya amince da batun cikin kyakkyawar zuciya ba tare da la’akari da doka ko haramcin dakatar da shi ba.

Ya ce:

“Na ce to, ba tare da la’akari da halacci ko haramcin batun ba, na yarda da abin da ya faru da zuciya daya kuma na dage kan yin duk abin da zan iya don tallafa wa jam’iyyar.”

Shahararren dan siyasar ya bayyana cewa zai ci gaba da kasancewa mai kwazo da tasiri a cikin APC tare da fatan samun nasarar jam’iyyar a babban zaben 2023.

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here