ƙasashen da Suka fi Taka Leda a Duniya

 

Hukumar ƙwallo ƙafa ta duniya FIFA ta saka Najeriya a matsayi na 36 na jerin ƙasashen da suka fi taka leda a duniya.

Cikin jadawalin da ta fitar ranar Alhamis, hukumar FIFA saka Najeriya a matsayi na huɗu a nahiyar Afirka.

Ƙasar Moroco ce ta farko a nahiyar Afirka, kuma ta 13 a duniya, yayin da Senegal ke matsayi na biyu a Afirka kuma ta 20 a duniya.

Masar ta 30 a duniya da Najeriya ta 36, da kuma Algeria ta 37 ne na uku da na huɗu da kuma na biyar a nahiyar Afirka.

Ƙasashen da ke kan gaba a duniya su ne Argentina da Faransa da Sifaniya da Ingila da Brazil.

 

 
VISIT OUR OTHER WEBSITES
PRNigeria.com EconomicConfidential.com Hausa.PRNigeria.com
EmergencyDigest.com PoliticsDigest.ng TechDigest.ng
HealthDigest.ng SpokesPersonsdigest.com TeensDigest.ng
ArewaAgenda.com Hausa.ArewaAgenda.com YAShuaib.com

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here