ƙasashen da Suka fi Taka Leda a Duniya
Hukumar ƙwallo ƙafa ta duniya FIFA ta saka Najeriya a matsayi na 36 na jerin ƙasashen da suka fi taka leda a duniya.
Cikin jadawalin da ta fitar ranar Alhamis, hukumar FIFA saka Najeriya a matsayi na huɗu a nahiyar Afirka.
Read Also:
Ƙasar Moroco ce ta farko a nahiyar Afirka, kuma ta 13 a duniya, yayin da Senegal ke matsayi na biyu a Afirka kuma ta 20 a duniya.
Masar ta 30 a duniya da Najeriya ta 36, da kuma Algeria ta 37 ne na uku da na huɗu da kuma na biyar a nahiyar Afirka.
Ƙasashen da ke kan gaba a duniya su ne Argentina da Faransa da Sifaniya da Ingila da Brazil.